Fadar shugaban kasa ta yi fatali da wata sanarwa da daya daga cikin bangarorin jamâiyyar APC reshen jihar Kano, ya yi na cewa, sun samu amincewar shugaban kasa Muhammadu Buhari.
A cikin wata sanarwa da babban mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Garba Shehu ya fitar a ranar Asabar, fadar shugaban kasar ta ce, Buhari bai amince da wani bangare ba, inda ya kara da cewa wannan magana ba gaskiya ba ce.
Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban kasar ya amince da daya daga cikin bangarorin APC a Kano.
âWannan ba gaskiya ba ne a fili. Wannan ba zai iya faruwa ba yayin da al’amura ke jiran shari’a daga kotuna. Don a fayyace wannan, shugaba Buhari bai amince da wani bangare ba. Goyon bayan sa na jamâiyyar APC ne a matsayin jamâiyya, hadin kai da karfi, ba na kowane bangare baâ. inji sanarwar fadar shugaban kasa.
Jaridar DAILY POST ta rawaito cewa hakan na zuwa ne kasa da mako guda bayan da gwamnatin jihar Kano ta musanta rade-radin da a ke yadawa cewa gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje da bangarensa na shirin sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa PRP.
Wannan jita-jita ta fito ne bayan wani taro da bangaren gwamnan na APC ya yi a yunkurin da kotun Abuja ta yanke na daukaka kara kan hukuncin da kotun Abuja ta yanke kan mazabun jamâiyyar da na kananan hukumomi da a ka gudanar a gidan gwamnatin jihar Kano a Africa House a ranar Lahadin da ta gabata.
Wata babbar kotun Abuja ta kori shugabannin jamâiyyar APC na Kano masu biyayya ga gwamna Ganduje tare da ayyana shugabannin tsohon gwamnan jihar Ibrahim Shekarau a matsayin zababben shugabannin jamâiyyar a jihar.