fidelitybank

APC Kano: Buhari bai amince da wani bangare ba – Fadar shugaban kasa

Date:

Fadar shugaban kasa ta yi fatali da wata sanarwa da daya daga cikin bangarorin jam’iyyar APC reshen jihar Kano, ya yi na cewa, sun samu amincewar shugaban kasa Muhammadu Buhari.

A cikin wata sanarwa da babban mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Garba Shehu ya fitar a ranar Asabar, fadar shugaban kasar ta ce, Buhari bai amince da wani bangare ba, inda ya kara da cewa wannan magana ba gaskiya ba ce.

Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban kasar ya amince da daya daga cikin bangarorin APC a Kano.

“Wannan ba gaskiya ba ne a fili. Wannan ba zai iya faruwa ba yayin da al’amura ke jiran shari’a daga kotuna. Don a fayyace wannan, shugaba Buhari bai amince da wani bangare ba. Goyon bayan sa na jam’iyyar APC ne a matsayin jam’iyya, hadin kai da karfi, ba na kowane bangare ba”. inji sanarwar fadar shugaban kasa.

Jaridar DAILY POST ta rawaito cewa hakan na zuwa ne kasa da mako guda bayan da gwamnatin jihar Kano ta musanta rade-radin da a ke yadawa cewa gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje da bangarensa na shirin sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa PRP.

Wannan jita-jita ta fito ne bayan wani taro da bangaren gwamnan na APC ya yi a yunkurin da kotun Abuja ta yanke na daukaka kara kan hukuncin da kotun Abuja ta yanke kan mazabun jam’iyyar da na kananan hukumomi da a ka gudanar a gidan gwamnatin jihar Kano a Africa House a ranar Lahadin da ta gabata.

Wata babbar kotun Abuja ta kori shugabannin jam’iyyar APC na Kano masu biyayya ga gwamna Ganduje tare da ayyana shugabannin tsohon gwamnan jihar Ibrahim Shekarau a matsayin zababben shugabannin jam’iyyar a jihar.

nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko Ĉ´anĈ™wallon...

Sunderland ta ɗauko Ĉ´anĈ™wallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan Ĉ™wallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ĉ˜ungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ĉ˜ungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp