fidelitybank

APC Kano: Buhari bai amince da wani bangare ba – Fadar shugaban kasa

Date:

Fadar shugaban kasa ta yi fatali da wata sanarwa da daya daga cikin bangarorin jam’iyyar APC reshen jihar Kano, ya yi na cewa, sun samu amincewar shugaban kasa Muhammadu Buhari.

A cikin wata sanarwa da babban mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Garba Shehu ya fitar a ranar Asabar, fadar shugaban kasar ta ce, Buhari bai amince da wani bangare ba, inda ya kara da cewa wannan magana ba gaskiya ba ce.

Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban kasar ya amince da daya daga cikin bangarorin APC a Kano.

“Wannan ba gaskiya ba ne a fili. Wannan ba zai iya faruwa ba yayin da al’amura ke jiran shari’a daga kotuna. Don a fayyace wannan, shugaba Buhari bai amince da wani bangare ba. Goyon bayan sa na jam’iyyar APC ne a matsayin jam’iyya, hadin kai da karfi, ba na kowane bangare ba”. inji sanarwar fadar shugaban kasa.

Jaridar DAILY POST ta rawaito cewa hakan na zuwa ne kasa da mako guda bayan da gwamnatin jihar Kano ta musanta rade-radin da a ke yadawa cewa gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje da bangarensa na shirin sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa PRP.

Wannan jita-jita ta fito ne bayan wani taro da bangaren gwamnan na APC ya yi a yunkurin da kotun Abuja ta yanke na daukaka kara kan hukuncin da kotun Abuja ta yanke kan mazabun jam’iyyar da na kananan hukumomi da a ka gudanar a gidan gwamnatin jihar Kano a Africa House a ranar Lahadin da ta gabata.

Wata babbar kotun Abuja ta kori shugabannin jam’iyyar APC na Kano masu biyayya ga gwamna Ganduje tare da ayyana shugabannin tsohon gwamnan jihar Ibrahim Shekarau a matsayin zababben shugabannin jam’iyyar a jihar.

bbc nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Ĉ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Ĉ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe Ĉ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aĈ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da Ĉ™ungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

ĈŠan takarar shugaban Ĉ™asa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp