fidelitybank

An tsige shugaban kwamitin tsaro a Kazakhstan a kan zanga-zanga man fetur

Date:

Shugaban kasar Kazakhstan ya tube guda daga cikin kusa a tafiyar sa a harkokin tsaron kasar daga mukaminsa na shugaban majalisar tsaron kasar a ranar Laraba, bayan da masu zanga-zangar suka kutsa kai tare da kona gine-ginen jama’a a wani rikici mafi muni da kasar ta shafe fiye da shekaru goma ana yi.

Majalisar ministocin ta yi murabus, amma hakan ya gaza kwantar da hankulan masu zanga-zangar bayan kwashe tsawon kwanaki a na tashe tashen hankula, sakamakon tashin farashin mai a kasar da ke hako mai a tsakiyar yankin Asiya.

Wasu masu zanga-zangar sun yi ta rera taken adawa da Nursultan Nazarbayev, mai shekaru 81, wanda ya ci gaba da rike madafun iko tun bayan da ya sauka a shekarar 2019 a matsayin wanda ya fi dadewa kan karagar mulki a tsohuwar kasar ta Soviet.

Wanda ya gaji Nazarbayev, shi ne shugaba, Kassym-Jomart Tokayev, ya ce, ya karbi ragamar jagorancin kwamitin tsaro mai karfi mukamin da Nazarbayev ya rike.

Har yanzu dai a na kallon tsohon shugaban a matsayin babban jigon siyasa a Nur-Sultan, babban birnin da a ka gina da sunan sa. An yi imanin danginsa suna sarrafa yawancin tattalin arzikin kasar.

 

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp