Shugaban kasar Kazakhstan ya tube guda daga cikin kusa a tafiyar sa a harkokin tsaron kasar daga mukaminsa na shugaban majalisar tsaron kasar a ranar Laraba, bayan da masu zanga-zangar suka kutsa kai tare da kona gine-ginen jama’a a wani rikici mafi muni da kasar ta shafe fiye da shekaru goma ana yi.
Majalisar ministocin ta yi murabus, amma hakan ya gaza kwantar da hankulan masu zanga-zangar bayan kwashe tsawon kwanaki a na tashe tashen hankula, sakamakon tashin farashin mai a kasar da ke hako mai a tsakiyar yankin Asiya.
Wasu masu zanga-zangar sun yi ta rera taken adawa da Nursultan Nazarbayev, mai shekaru 81, wanda ya ci gaba da rike madafun iko tun bayan da ya sauka a shekarar 2019 a matsayin wanda ya fi dadewa kan karagar mulki a tsohuwar kasar ta Soviet.
Wanda ya gaji Nazarbayev, shi ne shugaba, Kassym-Jomart Tokayev, ya ce, ya karbi ragamar jagorancin kwamitin tsaro mai karfi mukamin da Nazarbayev ya rike.
Har yanzu dai a na kallon tsohon shugaban a matsayin babban jigon siyasa a Nur-Sultan, babban birnin da a ka gina da sunan sa. An yi imanin danginsa suna sarrafa yawancin tattalin arzikin kasar.