fidelitybank

An kashe basarake tare da kona mutane 3 cikin tawagarsa a Ogun

Date:

Wasu mutane da suka nuna ba a sani ba sabo, sun kashe wani basarake tare da kona mutum uku a cikin ’yan tawagarsa da ransu a yankin Alagodo da ke Karamar Hukumar Ewekkoro ta Jihar Ogun.

Majiyar Aminiya ta ce, wasu ’yan daba ne suka tare Oba Ayinde Odetola ne tare da abokansa, suna dawowa daga rangadi, suka kashe shi sannan suka kona abokan nasa da ransu, bayan barkewar rikicin sarautar Alagodo da ke Kasar Egba.

Majiyar ta ce, tun bayan kisan da aka yi wa basaraken da abokan nasa da misalin karfe 11 na ranar Litinin, wasu mazauna yankin suka fara kaura daga garin.

Rikicin ya kunno kai ne bayan takaddama a kan wanda za a ba wa sauratar yankin a tsakanin ’yan kabilar Ake da kuma kabilar Owu da ke zaune a yankin na Kasar Egba.

Oba Ayinde Odetola da aka kashe dai dan kabilar Ake ne a Kasar Egba, inda wadansu mazauna suke bore a kan cewa babu yadda za a ayi dan kabilarsa ya mulki masarautar saboda ’yan kabilar Owu ne ke da rinjayen al’umma.

Majiyoyi a yankin Kasar Egba sun tabbatar mana cewa ko a kwanakin baya sai da aka yi wa wani kasin Oba Otedola kisan gilla a sakamakon rikicin.

Wata ’yar uwar Oba Odetola mai suna Cif Adenike Akintade, ta ce, “A ranar Litinin da safe aka sallamo ni daga asibiti, ga shi kuma na shiga halin juyayin rasuwar dan uwana da aka kashe da misalin karfe 11 na safe.

“Ranar Asabar Mai Martaba ya kira ni, cewa in rage wasu abubuwan da nake yi saboda gajiya na ira kara min rashin lafiyata.

“A watannin baya Oba Odetola ya rasa kaninsa a rikicin; ’yan daba ne suka kashe shi, ga shi yau kuma Mai Martaba ya bar duniya.”

A ranar Litinin da dare ne dai Kakakin Rundunar ’Yan Sanda na Jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi, ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya kara da cewa maharan sun kona motar basaraken bayan sun kashe shi.

Ya ce, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Ogun, Lanre Bankole tare da Mashawarcin Gwamna Dapo Abiodun, wato Olusola Subair, sun ziyarci garin domin gane wa kansu abin da ya faru.

A cewarsa, duk da cewa babu wanda aka kama a kan zargin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar ya umarci sashen ’yan sanda masu binciken laifukan kisa da ya gudanar da bincike a kan al’amarin.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp