fidelitybank

An kashe basarake tare da kona mutane 3 cikin tawagarsa a Ogun

Date:

Wasu mutane da suka nuna ba a sani ba sabo, sun kashe wani basarake tare da kona mutum uku a cikin ’yan tawagarsa da ransu a yankin Alagodo da ke Karamar Hukumar Ewekkoro ta Jihar Ogun.

Majiyar Aminiya ta ce, wasu ’yan daba ne suka tare Oba Ayinde Odetola ne tare da abokansa, suna dawowa daga rangadi, suka kashe shi sannan suka kona abokan nasa da ransu, bayan barkewar rikicin sarautar Alagodo da ke Kasar Egba.

Majiyar ta ce, tun bayan kisan da aka yi wa basaraken da abokan nasa da misalin karfe 11 na ranar Litinin, wasu mazauna yankin suka fara kaura daga garin.

Rikicin ya kunno kai ne bayan takaddama a kan wanda za a ba wa sauratar yankin a tsakanin ’yan kabilar Ake da kuma kabilar Owu da ke zaune a yankin na Kasar Egba.

Oba Ayinde Odetola da aka kashe dai dan kabilar Ake ne a Kasar Egba, inda wadansu mazauna suke bore a kan cewa babu yadda za a ayi dan kabilarsa ya mulki masarautar saboda ’yan kabilar Owu ne ke da rinjayen al’umma.

Majiyoyi a yankin Kasar Egba sun tabbatar mana cewa ko a kwanakin baya sai da aka yi wa wani kasin Oba Otedola kisan gilla a sakamakon rikicin.

Wata ’yar uwar Oba Odetola mai suna Cif Adenike Akintade, ta ce, “A ranar Litinin da safe aka sallamo ni daga asibiti, ga shi kuma na shiga halin juyayin rasuwar dan uwana da aka kashe da misalin karfe 11 na safe.

“Ranar Asabar Mai Martaba ya kira ni, cewa in rage wasu abubuwan da nake yi saboda gajiya na ira kara min rashin lafiyata.

“A watannin baya Oba Odetola ya rasa kaninsa a rikicin; ’yan daba ne suka kashe shi, ga shi yau kuma Mai Martaba ya bar duniya.”

A ranar Litinin da dare ne dai Kakakin Rundunar ’Yan Sanda na Jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi, ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya kara da cewa maharan sun kona motar basaraken bayan sun kashe shi.

Ya ce, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Ogun, Lanre Bankole tare da Mashawarcin Gwamna Dapo Abiodun, wato Olusola Subair, sun ziyarci garin domin gane wa kansu abin da ya faru.

A cewarsa, duk da cewa babu wanda aka kama a kan zargin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar ya umarci sashen ’yan sanda masu binciken laifukan kisa da ya gudanar da bincike a kan al’amarin.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp