fidelitybank

An kashe basarake tare da kona mutane 3 cikin tawagarsa a Ogun

Date:

Wasu mutane da suka nuna ba a sani ba sabo, sun kashe wani basarake tare da kona mutum uku a cikin ’yan tawagarsa da ransu a yankin Alagodo da ke Karamar Hukumar Ewekkoro ta Jihar Ogun.

Majiyar Aminiya ta ce, wasu ’yan daba ne suka tare Oba Ayinde Odetola ne tare da abokansa, suna dawowa daga rangadi, suka kashe shi sannan suka kona abokan nasa da ransu, bayan barkewar rikicin sarautar Alagodo da ke Kasar Egba.

Majiyar ta ce, tun bayan kisan da aka yi wa basaraken da abokan nasa da misalin karfe 11 na ranar Litinin, wasu mazauna yankin suka fara kaura daga garin.

Rikicin ya kunno kai ne bayan takaddama a kan wanda za a ba wa sauratar yankin a tsakanin ’yan kabilar Ake da kuma kabilar Owu da ke zaune a yankin na Kasar Egba.

Oba Ayinde Odetola da aka kashe dai dan kabilar Ake ne a Kasar Egba, inda wadansu mazauna suke bore a kan cewa babu yadda za a ayi dan kabilarsa ya mulki masarautar saboda ’yan kabilar Owu ne ke da rinjayen al’umma.

Majiyoyi a yankin Kasar Egba sun tabbatar mana cewa ko a kwanakin baya sai da aka yi wa wani kasin Oba Otedola kisan gilla a sakamakon rikicin.

Wata ’yar uwar Oba Odetola mai suna Cif Adenike Akintade, ta ce, “A ranar Litinin da safe aka sallamo ni daga asibiti, ga shi kuma na shiga halin juyayin rasuwar dan uwana da aka kashe da misalin karfe 11 na safe.

“Ranar Asabar Mai Martaba ya kira ni, cewa in rage wasu abubuwan da nake yi saboda gajiya na ira kara min rashin lafiyata.

“A watannin baya Oba Odetola ya rasa kaninsa a rikicin; ’yan daba ne suka kashe shi, ga shi yau kuma Mai Martaba ya bar duniya.”

A ranar Litinin da dare ne dai Kakakin Rundunar ’Yan Sanda na Jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi, ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya kara da cewa maharan sun kona motar basaraken bayan sun kashe shi.

Ya ce, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Ogun, Lanre Bankole tare da Mashawarcin Gwamna Dapo Abiodun, wato Olusola Subair, sun ziyarci garin domin gane wa kansu abin da ya faru.

A cewarsa, duk da cewa babu wanda aka kama a kan zargin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar ya umarci sashen ’yan sanda masu binciken laifukan kisa da ya gudanar da bincike a kan al’amarin.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp