Hukumar kula da lafiya a matakin farko ta jihar Kano, ta fara yin gangamin allurar rigakafin cutar Coronavirus (COVID-19) wadda take son yi wa mutane miliyan 3.4 a fadin jihar.
Tuni dai Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Jihar ta bayyana cewa, sama da mazauna Kano miliyan daya ne suka samu cikakkiyar allurar rigakafin, tun lokacin da aka fara allurar a Kano.
Sakataren zartarwa na hukumar, Dokta Tijani Husseini, ya bayyana hakan a yayin wani taron bita da aka shirya wa ma’aikatan yada labarai kan gangamin rigakafin cutar.
Tijjani, wanda shi ne daraktan Yaki da Cututtuka wanda, Dr. Imam Bello ya wakilce shi, ya musanta zargin kin amincewa da mutane ke bujurewa allurar COVID-19 a Kano.
Da yake jaddada cewa, an sami ci gaba sosai a yawan mutanen da suke karbar allurar, bisa radin kansu, Tijjani ya lura da cewa akwai karancin wayar da kan al’umma dangane da allurar..