Hukumar daƙile cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya, NCDC, ta ce, ƙarin mutum 230 ne suka kamu da cutar Korona a faɗin ƙasar a ranar Laraba 19 ga watan Janairun 2022.
Hukumar ta bayyana cewa, daga cikin sabbin wadanda suka kamu da cutar, jihar Legas ce a kan gaba, inda take da mutum 115, sai Gombe mai mutum 29, da Abuja mai 24.
A jihar Imo kuwa mutum 20 ne suka kamu, sai kuma Rivers inda aka samu karin mutane 10.
Yawan waɗanda suka kamu a sauran jihohin
Ondo-9 • Kano-5 • Abia-4 • Kaduna-4 • Oyo-4 • Kebbi-2 • Ogun-2 • Borno-1 • Jigawa-1
Yanzu dai adadin waɗanda suka kamu da cutar a Najeriya tun bayan ɓullarta ya kai 251,571, amma an sallami mutum 225,280 daga asibiti bayan sun warke.
Yawan waɗanda suka rasa rayukansu sanadin cutar ta korona kuwa ya kai 3,117.