Mutane da dama ciki da wajen Najeriya na ci gaba da nuna alhinin Hanifa ‘yar shekara 5 da malamin makarantar su ya kashe ta tare da binne ta a makarantar su.
cikin wadanda suka magantu a shafukan su na Twitter, akwai tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abukara wanda ya bayyana cewa, a gaggauta bi wa Hanifa hakinta, sakamakon samun mumunan labarin kisan gilla ga Hanifa ‘yar shekaru 5, bayan shafe kwanaki 47 a hannun masu garkuwa da mutane a Kano, ya ce”Wannan dabbanci ne da rashin imani ne” a cewar Atiku.
Shi kuwa Sanata Shehu Sani cewa ya yi, “Wanda ya aikta wannan mumunanan laifin ya girbi abun da ya shuka”
Audu Bulama Bakarki lauyan ne mai zaman kansa wanda ya ke a Birtaniya, ya ce“Mutumin ya tabbatar da laifin sa tare da karbar kudin fansa, bayan ya bata maganin Bera, dole ne a bi mata hakin ta”.
Adetutu Balogun cewa ta yi, “Yarinya ‘yar shekara 5 Hanifa an yi mata kisan gilla, wanda malamin ta ya aikata mata”.
Hanifa ta dai shafe tsawon kwanaki 47 ba a kara ganin duriyar ta ba, sai a jiya Alhamis da aka tabbatar da mutuwar ta.