fidelitybank

Al’umma na ci gaba da yin tofin Allah ya tsine a kan mutuwar Hanifa

Date:

Mutane da dama ciki da wajen Najeriya na ci gaba da nuna alhinin Hanifa ‘yar shekara 5 da malamin makarantar su ya kashe ta tare da binne ta a makarantar su.

cikin wadanda suka magantu a shafukan su na Twitter, akwai tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abukara wanda ya bayyana cewa, a gaggauta bi wa Hanifa hakinta, sakamakon samun mumunan labarin kisan gilla ga Hanifa ‘yar shekaru 5, bayan shafe kwanaki 47 a hannun masu garkuwa da mutane a Kano, ya ce”Wannan dabbanci ne da rashin imani ne” a cewar Atiku.

Shi kuwa Sanata Shehu Sani cewa ya yi, “Wanda ya aikta wannan mumunanan laifin ya girbi abun da ya shuka”

Audu Bulama Bakarki lauyan ne mai zaman kansa wanda ya ke a Birtaniya, ya ce“Mutumin ya tabbatar da laifin sa tare da karbar kudin fansa, bayan ya bata maganin Bera, dole ne a bi mata hakin ta”.

Adetutu Balogun cewa ta yi, “Yarinya ‘yar shekara 5 Hanifa an yi mata kisan gilla, wanda malamin ta ya aikata mata”.

Hanifa ta dai shafe tsawon kwanaki 47 ba a kara ganin duriyar ta ba, sai a jiya Alhamis da aka tabbatar da mutuwar ta.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naÉ—a shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp