Kasar Masar ta tsallake zuwa wasan zagayen kusa da na karshe na gasar AFCON na 2021, bayan ta doke kasar Cote di’ Voire da bugun daga kai sai mai tsaron raga.
Dan wasan Liverpool Mohammed Salah ne ya zura kwallon karshe, bayan da dan wasan Manchester United, Eric Bailly ya zubar da ta sa kwallon, wanda a ka yi 5 da 4.
A ranar Lahadi ne Masar za ta kara da Morocco a wasan daf da na kusa da na karshe.