Gwamnonin yankin Arewa maso Gabashin kasar nan, sun bukaci gwamnatin tarayya ta mayar da hankali wajen samar da wutar lantarki a yankin da a ke fama da matsalolin tsaro.
Sanarwar wanda shugaban kungiyar gwamnonin, gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum ya sanyawa hannu, ta ce,”Babbar matsalar da yankin ke fama da ita shi ne, rashin wutar lantarki, wanda hakan ke kawo koma baya ga bunkasa tattalin arziki tare da assasa rashin aikin yi sakamakon durkushewar kamfanoni. Rashin kammala aikin wuta na Dadin Kowa da Kashimbila, shi ne babban dalilin da ya jefa yankin cikin halin koma baya na tattalin arziki”.
Haka kuma gwamnonin sun yabawa gwamnatin tarayya bisa kokarin da ta ke yi wajen ganin yankin Arewa maso Gabas ya zauna lafiya.
Gwamnonin da su ka halarci taron sun hadar da gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum da gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni sai gwamna Inuwa Yahaya na jihar Gombe yayin da gwamnonin Bauchi da Adamawa da Taraba suka samu wakilcin mataimakan su.