fidelitybank

A na fakewa da biyan kuɗin fansa a ɗebe dukiyar gwamnati — Kwamishina

Date:

 

Kwamishinan Shari’a na Jihar Kwara, Salman Jawando ya yi zargin cewa “a na ɗebe kuɗaɗen gwamnati bayan fakewa da cewa dole a bayar da kuɗin fansa ga masu garkuwa da mutane sannan su saki waɗanda su ka kama.”
Jawando ya yi wannan zargi ne a ranar Litinin a yayin taron ranar Shari’a na 2021/2022 da kuma bikin sallamar alaƙalan da su ka yi murabus da ga aiki a Ilori.
Jawando ya bi sahun waɗanda su ke kira da a yi wa ɗaukacin fannin Shari’a garambawul a Nijeriya.
“Rashin tsaro a ƙasar nan ya yi ƙamari har ta kai ga ba wan da ya ke yin Bacci da ido biyu a rufe,” in ji shi.
“Batun kuɗin fansa ga masu garkuwa da mutane ya zamo wata hanya 5a samun maƙudan kuɗaɗe da ɓatagari su ke yi da haɗin kan wasu mugayen mutane.
“Ya zamo wata hanya da a ke kwashe kuɗaɗen gwamnati inda a ke fakewa da biyan kuɗin fansa da ƙaryar cewa wai idan ba a biya ba to waɗanda a ka sace ɗin za su shiga uku.
“Ɓangaren Shari’a wanda ya zamana nan ne madogarar talaka a ƙasar nan ya kamata ya tashi ya yi tashi tsaye domin tserar da ƴan ƙasa da ga wannan bala’in da ke cinye tsokokin jikkunan mu,” in ji Jawando.
Kwamishinan ya nuna mamaki da yadda a ke jan ƙafa a shari’ar masu garkuwa da mutane, inda ya baiyana cewa hakan na nuni da cewa dole a yi garambawul a gaba ɗaya ɓangaren Shari’a a ƙasar nan.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp