fidelitybank

A na fakewa da biyan kuɗin fansa a ɗebe dukiyar gwamnati — Kwamishina

Date:

 

Kwamishinan Shari’a na Jihar Kwara, Salman Jawando ya yi zargin cewa “a na ɗebe kuɗaɗen gwamnati bayan fakewa da cewa dole a bayar da kuɗin fansa ga masu garkuwa da mutane sannan su saki waɗanda su ka kama.”
Jawando ya yi wannan zargi ne a ranar Litinin a yayin taron ranar Shari’a na 2021/2022 da kuma bikin sallamar alaƙalan da su ka yi murabus da ga aiki a Ilori.
Jawando ya bi sahun waɗanda su ke kira da a yi wa ɗaukacin fannin Shari’a garambawul a Nijeriya.
“Rashin tsaro a ƙasar nan ya yi ƙamari har ta kai ga ba wan da ya ke yin Bacci da ido biyu a rufe,” in ji shi.
“Batun kuɗin fansa ga masu garkuwa da mutane ya zamo wata hanya 5a samun maƙudan kuɗaɗe da ɓatagari su ke yi da haɗin kan wasu mugayen mutane.
“Ya zamo wata hanya da a ke kwashe kuɗaɗen gwamnati inda a ke fakewa da biyan kuɗin fansa da ƙaryar cewa wai idan ba a biya ba to waɗanda a ka sace ɗin za su shiga uku.
“Ɓangaren Shari’a wanda ya zamana nan ne madogarar talaka a ƙasar nan ya kamata ya tashi ya yi tashi tsaye domin tserar da ƴan ƙasa da ga wannan bala’in da ke cinye tsokokin jikkunan mu,” in ji Jawando.
Kwamishinan ya nuna mamaki da yadda a ke jan ƙafa a shari’ar masu garkuwa da mutane, inda ya baiyana cewa hakan na nuni da cewa dole a yi garambawul a gaba ɗaya ɓangaren Shari’a a ƙasar nan.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp