Kotun shariar musulinci mai zaman ta a Ungogo karkashin mai shari’a, Mansur Ibrahim, ta tsayar da ranar 12 ga watan Janairu, domin ci gaba da sauraron shaidu a kunshin zargin da ‘yansanda ke yi wa dagacin Dausayi, Malam Abba Muhammad Dausayi da Sulaiman Muhammad da Amina Sulaiman bisa zargin hada baki da cuta da kuma kutse.
Ma su korafi iyalan, Alhaji Sharif Fillo Goron Dutse sun bayyanawa kotun cewar, dagacin Dausayi Malam Abba Muhammad, ya hada baki da mutane 2 sun sayar da wasu gonaki 3 mallakar, Alhaji Sharif Fillo.
Sai dai a zaman kotun an saurari shaidar ma su kara wanda malamin gandun daji ne, ya kuma fayyacewa kotun dukkan abin da ya sa ni sai dai lauyan wadanda a ke tuhumar ya bukaci shaidar ya gabatar da wata takarda da ya ambata a kan yadda jami’ar Bayero ta sanya su aikin fitar da taswirar gonakin.