fidelitybank

Zulum ya ziyarci Chibok bayan hari da aka kai

Date:

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ziyarci garin Chibok ranar Litinin, bayan wani harin da aka kai kan wasu al’umomi uku na karamar hukumar.

Yayin ziyarar, Gwamna Zulum ya gana da iyalan mata 22 da maza biyu da mayakan Boko Haram/ISWAP suka sace a Kawtakare, Korohuma da kuma Pemi yayin harin da suka kai.

Mayakan sun kai wannan harin ne a Kawtakare ranar 21 ga watan Janairu, 2022, inda kuma suka kai wani harin ranar 14 ga watan na Janairu bayan na ranar 30 ga watan Disambar bara da suka kai kan al’ummar Korohuma.

Gwamnan ya ce, “Mun zo Chibok ne domin yi muku jaje, musamman ‘yan uwan wadanda aka sace da ‘yan uwanmu mutum hudun da mayakan Boko Haram suka kashe.”

Gwamnan ya kuma ce gwamnatin jihar ta ji zafin al’amarin da ya auku kuma ya yi alkawarin haka ba zai sake aukuwa ba.

Gwamna Zulum ya lura cewa kananan hukumomin Biu da Askira da Chibok da kuma Damboa ne suka fi shan wahalar jerin hare-haren da kungiyoyin Boko Haram da ISWAP ke kai wa yankin.

Ya kuma ce gwamnatinsa ba za ta gaza ba wajen bai wa jami’an tsaro taimakon da suke bukata domin kawo karshen wannan al’amarin.Yayin da yake nasa jawabin, shugaban karamar hukumar ta Chibok Umar Ibrahim ya ce baya ga mutum 24 da aka sace, da mutum hudun da suka rasa rayukansu, maharan sun kona gine-gine 110, wadanda suka hada da gidaje 73 da shaguna 33 da kuma coci-coci guda hudu.

Akwai kuma motocin hawa takwas da kekuna uku da su ma mayakan suka kona.

Gwamnan na Borono ya umarci karamar hukumar ta tattara bayanan ainihin barnar da aka yi wa al’umomin uku sannan su mika masa cikakken rahoton. A cewar BBC.

latest news in lokoja, kogi state

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na É—aukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Æ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Æ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Æ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

ÆŠan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp