fidelitybank

Zulum ya ziyarci Chibok bayan hari da aka kai

Date:

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ziyarci garin Chibok ranar Litinin, bayan wani harin da aka kai kan wasu al’umomi uku na karamar hukumar.

Yayin ziyarar, Gwamna Zulum ya gana da iyalan mata 22 da maza biyu da mayakan Boko Haram/ISWAP suka sace a Kawtakare, Korohuma da kuma Pemi yayin harin da suka kai.

Mayakan sun kai wannan harin ne a Kawtakare ranar 21 ga watan Janairu, 2022, inda kuma suka kai wani harin ranar 14 ga watan na Janairu bayan na ranar 30 ga watan Disambar bara da suka kai kan al’ummar Korohuma.

Gwamnan ya ce, “Mun zo Chibok ne domin yi muku jaje, musamman ‘yan uwan wadanda aka sace da ‘yan uwanmu mutum hudun da mayakan Boko Haram suka kashe.”

Gwamnan ya kuma ce gwamnatin jihar ta ji zafin al’amarin da ya auku kuma ya yi alkawarin haka ba zai sake aukuwa ba.

Gwamna Zulum ya lura cewa kananan hukumomin Biu da Askira da Chibok da kuma Damboa ne suka fi shan wahalar jerin hare-haren da kungiyoyin Boko Haram da ISWAP ke kai wa yankin.

Ya kuma ce gwamnatinsa ba za ta gaza ba wajen bai wa jami’an tsaro taimakon da suke bukata domin kawo karshen wannan al’amarin.Yayin da yake nasa jawabin, shugaban karamar hukumar ta Chibok Umar Ibrahim ya ce baya ga mutum 24 da aka sace, da mutum hudun da suka rasa rayukansu, maharan sun kona gine-gine 110, wadanda suka hada da gidaje 73 da shaguna 33 da kuma coci-coci guda hudu.

Akwai kuma motocin hawa takwas da kekuna uku da su ma mayakan suka kona.

Gwamnan na Borono ya umarci karamar hukumar ta tattara bayanan ainihin barnar da aka yi wa al’umomin uku sannan su mika masa cikakken rahoton. A cewar BBC.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naÉ—a shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp