fidelitybank

Zulum ya ziyarci Chibok bayan hari da aka kai

Date:

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ziyarci garin Chibok ranar Litinin, bayan wani harin da aka kai kan wasu al’umomi uku na karamar hukumar.

Yayin ziyarar, Gwamna Zulum ya gana da iyalan mata 22 da maza biyu da mayakan Boko Haram/ISWAP suka sace a Kawtakare, Korohuma da kuma Pemi yayin harin da suka kai.

Mayakan sun kai wannan harin ne a Kawtakare ranar 21 ga watan Janairu, 2022, inda kuma suka kai wani harin ranar 14 ga watan na Janairu bayan na ranar 30 ga watan Disambar bara da suka kai kan al’ummar Korohuma.

Gwamnan ya ce, “Mun zo Chibok ne domin yi muku jaje, musamman ‘yan uwan wadanda aka sace da ‘yan uwanmu mutum hudun da mayakan Boko Haram suka kashe.”

Gwamnan ya kuma ce gwamnatin jihar ta ji zafin al’amarin da ya auku kuma ya yi alkawarin haka ba zai sake aukuwa ba.

Gwamna Zulum ya lura cewa kananan hukumomin Biu da Askira da Chibok da kuma Damboa ne suka fi shan wahalar jerin hare-haren da kungiyoyin Boko Haram da ISWAP ke kai wa yankin.

Ya kuma ce gwamnatinsa ba za ta gaza ba wajen bai wa jami’an tsaro taimakon da suke bukata domin kawo karshen wannan al’amarin.Yayin da yake nasa jawabin, shugaban karamar hukumar ta Chibok Umar Ibrahim ya ce baya ga mutum 24 da aka sace, da mutum hudun da suka rasa rayukansu, maharan sun kona gine-gine 110, wadanda suka hada da gidaje 73 da shaguna 33 da kuma coci-coci guda hudu.

Akwai kuma motocin hawa takwas da kekuna uku da su ma mayakan suka kona.

Gwamnan na Borono ya umarci karamar hukumar ta tattara bayanan ainihin barnar da aka yi wa al’umomin uku sannan su mika masa cikakken rahoton. A cewar BBC.

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp