fidelitybank

Mutane 8 sun mutu yayin shiga filin wasa a Kamaru

Date:

Rahotanni na nuni da cewa, akalla mutune takwas ake zargin sun mutu yayin da 38 suka jikkata, sakamakon wani turmutsitsi da ya auku a wajen filin da ake buga gasar cin kofin nahiyar Afirka ta Afcon a Kamaru.

Hotunan bidiyo sun nuna yadda ‘yan kallo suka rinÆ™a kokowar shiga fili wasa na Paul Biya da ke birnin Yaounde.

Naseri Paul Biya, wanda shi ne gwamnan yankin tsakiyar Kamaru, ya ce akwai yiwuwar a samu karin mutanen da abin ya shafa, a cewar kamfanin labarai na AP.

Wani rahoton kuma na cewa akwai yara da dama da suka suma.

Filin wasan na iya daukar mutum dubu 60, amma saboda matakan da ake É—auka saboda annobar korona ba a yarda a haura kashi 80 cikin 100 na wannan adadin ba.

Jami’ai sun ce mutum dubu 50 ne suka yi kokarin shiga filin wasan domin kallo.

Malaman jinya Olinga Prudence ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na AP cewa, wasu daga cikin mutanen da suka jikkata na cikin yanayi na galabaita.

Hukumar kwallon kasashen Afirka, CAF a wata sanarwa ta ce tana bincike kan lamarin domin samun ƙarin bayanai kan ainihin abin da ya faru.

An dai fafata a zagaye na biyu na gasar tsakanin Cameroon da Comoros duk da faruwar wannan al’amari, kuma mai karban bakwancin wasan ta yi nasara da 2-1.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miÆ™a saÆ™on ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe Æ´an É—aurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin Æ´an Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama Æ´an Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na Æ™asa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp