fidelitybank

2023: Za a rantsar da ni a matsayin sabon gwamnan Kaduna – Sanata Shehu Sani

Date:

Shahararren dan siyasar Najeriya, Sanata Shehu Sani ya bayyana aniyarsa na maye gurbin gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna a 2023.

Naija News ta rawaito cewa tsohon Sanatan Kaduna ta tsakiya ya bayyana haka ne a ranar Asabar a wata hira da ya yi da gidan rediyon Invicta FM.

Shehu ya ce, dalilin da ya sa ya shiga takarar gwamnan jihar a 2023 shi ne, domin tsaftace sharar da gwamna El-Rufai ya shigo da shi jihar tare da tabbatar da tsaron jama’a.

Tsohon Sanatan ya ce, gwamnan ya gaza wajen tabbatar da rayuka da dukiyoyin al’ummar da ya rantse a lokacin rantsar da shi a shekarar 2015.

Ya kara da cewa El-Rufai bai cancanci ya hau mulki ba, saboda ya kasa daukar rayukan al’ummar jihar da matukar muhimmanci.

Ya ce: “Mun zauna da magoya bayana, kuma suna son in tsaya takarar gwamnan jihar Kaduna, wanda zan yi domin kawar da APC, in Allah Ya yarda; a tsige zababben dan takarar gwamnan jihar sannan na shiga gidan gwamnati inda za a rantsar da Kwamared a matsayin gwamnan da zai kawo sauye-sauye, wanda zai share duk wata kazantar da suka kawo jihar da sunan ci gaba.”

“Zan kawo tsaro. Wannan shi ne abin da magoya bayana su ka so kuma na amince da su. Domin haka zan tsaya takarar gwamna a karkashin jam’iyyar PDP. Domin haka ina kira ga al’ummar Kaduna da su ba ni goyon baya, su ba ni hadin kai.

“Ina kuma rokon addu’o’insu; Ina bukatan addu’ar malaman addini, ‘yan kasuwa, nakasassu, mata da matasa. Kun zabi Malam a matsayin Gwamna abin da ya rage a yanzu shi ne a samu abokin zama a matsayin gwamna domin ganin bambancin da ke tsakaninmu.

“Dole ne ku ƙi shafaffu ɗan takarar waɗanda suka rushe gidajenku. Ku tallafa mana don ganin yadda za mu kafa gwamnati mai mutunta ra’ayin talakawan jihar.”

Da ya ke magana kan rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar PDP a jihar, Sani ya yi kira ga shugabannin jam’iyyar da su hada kan ‘ya’yan jam’iyyar gabanin zaben gwamna na 2023.

Tsohon dan majalisar ya kuma bukaci jam’iyyar adawa da su tabbatar sun kafa gwamnati da za ta mutunta ra’ayin talakawan jihar.

Sani ya kara da cewa a matsayinsa na dan takara ba shi da kudin da zai raba wa delegates su zabe shi, inda ya kara da cewa idan talaka ya yanke shawarar zabar shi da kudi ko ba tare da shi ba, zai yi nasara.

Sai dai ya gargadi jama’a cewa siyasar kudi ita ce ta kawo kasar cikin “rikici a karkashin jam’iyya mai mulki”. Inji Sanata Shehu Sani.

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp