fidelitybank

2023: Za a rantsar da ni a matsayin sabon gwamnan Kaduna – Sanata Shehu Sani

Date:

Shahararren dan siyasar Najeriya, Sanata Shehu Sani ya bayyana aniyarsa na maye gurbin gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna a 2023.

Naija News ta rawaito cewa tsohon Sanatan Kaduna ta tsakiya ya bayyana haka ne a ranar Asabar a wata hira da ya yi da gidan rediyon Invicta FM.

Shehu ya ce, dalilin da ya sa ya shiga takarar gwamnan jihar a 2023 shi ne, domin tsaftace sharar da gwamna El-Rufai ya shigo da shi jihar tare da tabbatar da tsaron jama’a.

Tsohon Sanatan ya ce, gwamnan ya gaza wajen tabbatar da rayuka da dukiyoyin al’ummar da ya rantse a lokacin rantsar da shi a shekarar 2015.

Ya kara da cewa El-Rufai bai cancanci ya hau mulki ba, saboda ya kasa daukar rayukan al’ummar jihar da matukar muhimmanci.

Ya ce: “Mun zauna da magoya bayana, kuma suna son in tsaya takarar gwamnan jihar Kaduna, wanda zan yi domin kawar da APC, in Allah Ya yarda; a tsige zababben dan takarar gwamnan jihar sannan na shiga gidan gwamnati inda za a rantsar da Kwamared a matsayin gwamnan da zai kawo sauye-sauye, wanda zai share duk wata kazantar da suka kawo jihar da sunan ci gaba.”

“Zan kawo tsaro. Wannan shi ne abin da magoya bayana su ka so kuma na amince da su. Domin haka zan tsaya takarar gwamna a karkashin jam’iyyar PDP. Domin haka ina kira ga al’ummar Kaduna da su ba ni goyon baya, su ba ni hadin kai.

“Ina kuma rokon addu’o’insu; Ina bukatan addu’ar malaman addini, ‘yan kasuwa, nakasassu, mata da matasa. Kun zabi Malam a matsayin Gwamna abin da ya rage a yanzu shi ne a samu abokin zama a matsayin gwamna domin ganin bambancin da ke tsakaninmu.

“Dole ne ku ƙi shafaffu ɗan takarar waɗanda suka rushe gidajenku. Ku tallafa mana don ganin yadda za mu kafa gwamnati mai mutunta ra’ayin talakawan jihar.”

Da ya ke magana kan rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar PDP a jihar, Sani ya yi kira ga shugabannin jam’iyyar da su hada kan ‘ya’yan jam’iyyar gabanin zaben gwamna na 2023.

Tsohon dan majalisar ya kuma bukaci jam’iyyar adawa da su tabbatar sun kafa gwamnati da za ta mutunta ra’ayin talakawan jihar.

Sani ya kara da cewa a matsayinsa na dan takara ba shi da kudin da zai raba wa delegates su zabe shi, inda ya kara da cewa idan talaka ya yanke shawarar zabar shi da kudi ko ba tare da shi ba, zai yi nasara.

Sai dai ya gargadi jama’a cewa siyasar kudi ita ce ta kawo kasar cikin “rikici a karkashin jam’iyya mai mulki”. Inji Sanata Shehu Sani.

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp