fidelitybank

Ƴan ta’adda sun ƙona fasinjoji 42 a cikin mota a Sokoto inda 37 su ka rasu nan take

Date:

 

Rahotanni daga Jihar Sokoto sun baiyana cewa ƴan ta’adda sun ƙona wata motar fasinja ɗauke da mutum 42.

Rahotanni sun baiyana cewa mutum 37 sun ƙone ƙurmus, inda biyar kuma su ka tsira da raunuka daban-daban.

BBC Hausa ta rawaito cewa fasinjojin sun fito ne daga Ƙaramar Hukumar Sabon Birni da ke jihar domin yin ƙaura zuwa wasu yankunan Najeriya, saboda ta’azzarar ayyukan ƴan bindiga a inda suke.

Wasu shaidu sun cewa BBC Hausa cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 9 na safiyar ranar Litinin.

“Motar ɗauke da fasinjojin ta tashi daga Sabon Birni, ta yi tafiyar da bai fi kilomita shida ba zuwa kauyen Gidan Bawa inda wannan masifa ta afka mata,” kamar yadda waɗanda suka yi aikin ceton suka bayyana wa BBC.

Tuni dai aka yi jana’ziar mamatan in ji shaidu.

Wani ganau ya cewa BBC: “Lokacin da abin ya faru ina Sabon Birni aka kira ni aka shaida min. Daga cikin matafiyan ma har da wani ƙanin mahaifiyata da matarsa da ƴaƴansu huɗu.

“Cikin ƴaƴan Allah Ya yi wa biyu rasuwa. Lokacin da muka isa wajen da ya faru mun je mun iske mutane sun mutu, kuma a ƙalla mun ƙirga gawarwaki sun kai 25,” ya ce.

Ya ƙara da cewa akwai tsirarun mutane daga cikinsu da suka tsira.

Shi ma wani shaidan da ya buƙaci a sakaya sunansa ya ce “mutum 45 ne a cikin motar, amma bakwai ne suka tsira da rayukansu, su ma a yanzu haka suna cikin halin ha’ula’i.

“Babu maganar ma ka ga gawa a kammale, sai dai muka dinga haɗa ƙafafu da hannaye daban-daban aka yi musu jana’iza a tare.”

Ya ce shi yana tsaye a tasha ma lokacin da motar ta tashi. “Ƴan Union ne ma na tasha suka gaya mana adadin mutanen da motar ta tashi da su,” a cewarsa.

Yankin arewa maso yammacin Najeriya na ɗaya daga cikin yankunan da suka fi fama da matsalar tsaro a Najeriya, sai dai a lokuta da dama gwamnatocin yankin na cewa suna iya kokarinsu domin tabbatar da kare rayuka da dukiyoyin al’umarsu, abin da al’umar ke cewa ba sa gani a kasa.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp