fidelitybank

Ƴan sanda sun kama mutum 4 a zanga-zangar masu kiwon zuma a ƙasar Chile

Date:

Ƴan Sanda a ƙasar Chile sun kama mutum huɗu da ga cikin masu kiwon zuma da bayan da su ka yi zanga-zanga a fadar shugaban ƙasa a Santiago.
Kamfanin Daillancin Labarai na Reuters ya rawaito cewa masu kiwon zumar, a ƙarƙashin ƙungiyar su, sun girke kwangin zuma kusan 60 mai ɗauke da ƙudan zuma kimanin dubu 10 a ciki.
Bayan da su ka fara zanga-zangar ne sai ƙudan zuman su ka fara tasowa, inda su kai kan me-uwa-da-wabi su ka riƙa gasawa ƴan sandan cizo.
Rahotanni dai sun baiyana cewa ƴan sanda 7 ne su ka sha cizon ƙudan zumar, inda saura kuma su ka ranta a na kare.
Farin da ƙasar ta shiga ne tun shekarar 2010 ya shafi noman zuma a ƙasar, sakamakon fulawowi da tsirrai da ciyawu ba sa fitowa saboda rashin ruwa inda kuma su ne abincin da zuma ke ci ta rayu.
Ƴan ƙungiyar sun koka cewa farin na sanyawa kudan zuma na mutuwa kuma yawan su na raguwa, in da su ka nuna cewa mutuwar ƙudan zuma ɗaya, illa ce ga duniya baki daya.
Masu zanga-zangar, waɗanda su ka rufe wasu manyan titunan birnin sun yi kira ga gwamnati da ta farfaɗo da noman zuma domin tattalin arzikin manoman ya dawo.
Sun kuma nemi su gana da shugaban ƙasar Chile, Sebastian Pinera.
A halin yanzu dai, tuni ƴan sanda su ka cafke mutane huɗu a cikin masu zanga-zangar.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp