fidelitybank

Ƴan sanda sun kama mutum 4 a zanga-zangar masu kiwon zuma a ƙasar Chile

Date:

Ƴan Sanda a ƙasar Chile sun kama mutum huɗu da ga cikin masu kiwon zuma da bayan da su ka yi zanga-zanga a fadar shugaban ƙasa a Santiago.
Kamfanin Daillancin Labarai na Reuters ya rawaito cewa masu kiwon zumar, a ƙarƙashin ƙungiyar su, sun girke kwangin zuma kusan 60 mai ɗauke da ƙudan zuma kimanin dubu 10 a ciki.
Bayan da su ka fara zanga-zangar ne sai ƙudan zuman su ka fara tasowa, inda su kai kan me-uwa-da-wabi su ka riƙa gasawa ƴan sandan cizo.
Rahotanni dai sun baiyana cewa ƴan sanda 7 ne su ka sha cizon ƙudan zumar, inda saura kuma su ka ranta a na kare.
Farin da ƙasar ta shiga ne tun shekarar 2010 ya shafi noman zuma a ƙasar, sakamakon fulawowi da tsirrai da ciyawu ba sa fitowa saboda rashin ruwa inda kuma su ne abincin da zuma ke ci ta rayu.
Ƴan ƙungiyar sun koka cewa farin na sanyawa kudan zuma na mutuwa kuma yawan su na raguwa, in da su ka nuna cewa mutuwar ƙudan zuma ɗaya, illa ce ga duniya baki daya.
Masu zanga-zangar, waɗanda su ka rufe wasu manyan titunan birnin sun yi kira ga gwamnati da ta farfaɗo da noman zuma domin tattalin arzikin manoman ya dawo.
Sun kuma nemi su gana da shugaban ƙasar Chile, Sebastian Pinera.
A halin yanzu dai, tuni ƴan sanda su ka cafke mutane huɗu a cikin masu zanga-zangar.

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp