fidelitybank

Ƴan Sanda sun cafke tsohon Kwamishinan Ganduje kuma ɗan adawar sa

Date:

‘Yan Sanda sun kama Muaz Magaji, ɗaya daga cikin masu sukar gwamnan Jihar Kano Abdullahi Ganduje.
Ƴan sanda sun kama shi ne bayan wata hira da aka yi da shi kai tsaye a gidan talabijin na Trust TV da ke Utako, Abuja da misalin karfe 9:15 na dare.
Ko da yake har yanzu ƴan sanda ba su ce uffan ba kan kamun nasa, shaidun gani da ido  sun shaida wa jaridar DAILY NIGERIAN cewa jami’an ƴan sanda sun biyo Magaji a baya bayan ya bar ofishin gidan talabijin ɗin.
“Bayan ‘yan mintoci da suka gabata wani abin takaici, damuwa da nadama ya faru a hanyar Ngozi Okonjo Iwela ta hanyar TOS Benson Crescent junction. Injiniya Magaji Muazu ya yi hatsari ne inda a ka hankaɗa motarsa ​​kirar Honda ta sauka daga kan titin sannan ta daki wata sandar fitilar titi. Duk da cewa ya fito daga cikin motar bai ji rauni ba, amma duk jakunkunan Airbags sun fito waje.
“Da alama aikin ‘yan sanda ne domin nan take su ka kama shi su ka kai shi caji-ofis na Utako da ƙarfin tsiya. Yayin da nake rubuta wannan bayani na kasance a wurin ina tsare motarsa ​​kuma yanzu muna kan hanyarmu ta zuwa ofishin ‘yan sanda. Jakarsa da batirin motarsa ​​suna tare da ni,” inji wani ganau.
A tuna cewa a ranar 17 ga watan Janairu, ‘yan sanda a Kano sun gayyaci Magaji domin ya amsa tambayoyi dangane da karar da aka shigar a kan sa.
Sai ya aika lauyoyinsa zuwa ga rundunar maimakon ya bayyana a gabansu da kan sa, sannan ya shigar da kara na tabbatar da tsaro a kan ‘yan sanda.
Ganduje ya kori Magaji, wanda tsohon kwamishinan ayyuka da aiyukan more rayuqa saboda “kalaman rashin ɗa’a” da ya yi kan rasuwar shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Abba Kyari.
Tun bayan barin gwamnati, tsohon kwamishinan ya rika sukar gwamnan kan salon shugabancinsa da kuma shigar da iyalansa cikin harkokin mulki a jihar.
Biyo bayan fitowar bangaren jam’iyyar APC a jihar na Sanata Shekarau, sai tsohon kwamishinan ya koma bangaren.

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai...

Falana ya caccaki Tinubu kan salon tattalin arzikin Najeriya

Fitaccen lauyan nan mai kare haƙƙin bil adama, Femi...

Yahudawa sun yiwa Netanyahu tutsu kan mamaye Gaza

Ƴan'uwan Isra'ilawan da aka yi garkuwa da su a...

Cin zarafin Daliba ya sanya yin zanga-zanga a China

Zanga-zanga ta ɓarke a kudancin China sakamakon cin zarafin...

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...
X whatsapp