fidelitybank

Ƴan Isra’ila da a ka fara saki sun koma gida

Date:

Hukumomin sojin Isra’ila sun tabbatar da cewa mata ukun nan da Hamas ta saki a cikin ‘yan ƙasar da ta yi garkuwa da su, yanzu sun koma Isra’ila daga Gaza.

A ɗazu ne Hamas ta danka matan ga ƙungiyar agaji ta duniya ta Red Cross, inda ‘yan Isra’ila da dama suka yi maraba tare da murna da sakin nasu, wanda suka kalla ta wani babban allon talabijin da aka girke a babban birnin Isra’ilar Tel Aviv.

Bayan an duba lafiyarsu da da farko daga nan za a tafi da su wani asibiti a kusa da babban birnin kafin kuma daga bisani a haɗa su da iyalansu.

An tabbatar da matan su ne waɗanda Hamas ta bayar da sunansu a waɗanda za ta fara saki – Doron Steinbrecher, da Romi Gonen da kuma Emily Damari.

Kakakin sojin Isra’ila Daniel Hagari a wani taron manema labarai ya ce a cikin wannan mako shida na farko za a rika sakin mutum uku ko hudu duk mako cikin wadanda Hamas ɗin ta yi garkuwa da su.

Wani jami’in Hamas ɗin ya sheda wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa a ranar Asabar za a yi musayar fursunonin ta gaba

Akwai ƙarin mutum 30 da Hamas ɗin za ta saki, rukuni-rukuni a cikin mako shida inda za a riƙa musayarsu da ɗaruruwan Falasɗinawa da ke gidajen yarin Isra’ila.

Motocin Red Cross

Asalin hoton,Reuters

A yau ɗin ne kuma yayin da Hamas ke sakin ‘yan Isra’ilar uku aka ga motocin safa-safa na Red Cross a wajen gidan yari na Ofer da ke yankin Gabar Yamma da Isra’ila ta mamaye, sun je domin ɗaukar fursunoni Falasɗinawa.

Hamas ta ce a duk mutum ɗaya da ta saki na Isra’ila za a saki Falasɗinawa 30 fursunoni daga gidan yarin Isra’ila.

A ranar 7 ga watan Oktoba na 2023 me Hamas ta kai wa Isra’ila wani harin bazata inda ta kashe kusan mutum 1,200 ta kuma yi garkuwa da 251 da ta kai Gaza. A cewar BBC.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...

Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta

Ƙasashen Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta...

Yansanda sun kama Sojoji cikin ‘ƴan ƙungiyar asiri’ a jihar Ogun

Rundunar 'yansanda reshen jihar Ogun, ta tabbatar da kama...

Yadda ambaliya ta shanye Adamawa

Rahotonni daga birnin Yola na jihar Adamawa na cewa,...

Yadda Jodan da Dubai ke jefa wa al’ummar Gaza abinci ta sama

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Jordan ta ce, jiragen...

Tarihi ba zai manta da Najeriya ba a bangaren kwallon kafar Mata

Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo...

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...
X whatsapp