fidelitybank

Ƴan Isra’ila da a ka fara saki sun koma gida

Date:

Hukumomin sojin Isra’ila sun tabbatar da cewa mata ukun nan da Hamas ta saki a cikin ‘yan ƙasar da ta yi garkuwa da su, yanzu sun koma Isra’ila daga Gaza.

A ɗazu ne Hamas ta danka matan ga ƙungiyar agaji ta duniya ta Red Cross, inda ‘yan Isra’ila da dama suka yi maraba tare da murna da sakin nasu, wanda suka kalla ta wani babban allon talabijin da aka girke a babban birnin Isra’ilar Tel Aviv.

Bayan an duba lafiyarsu da da farko daga nan za a tafi da su wani asibiti a kusa da babban birnin kafin kuma daga bisani a haɗa su da iyalansu.

An tabbatar da matan su ne waɗanda Hamas ta bayar da sunansu a waɗanda za ta fara saki – Doron Steinbrecher, da Romi Gonen da kuma Emily Damari.

Kakakin sojin Isra’ila Daniel Hagari a wani taron manema labarai ya ce a cikin wannan mako shida na farko za a rika sakin mutum uku ko hudu duk mako cikin wadanda Hamas ɗin ta yi garkuwa da su.

Wani jami’in Hamas ɗin ya sheda wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa a ranar Asabar za a yi musayar fursunonin ta gaba

Akwai ƙarin mutum 30 da Hamas ɗin za ta saki, rukuni-rukuni a cikin mako shida inda za a riƙa musayarsu da ɗaruruwan Falasɗinawa da ke gidajen yarin Isra’ila.

Motocin Red Cross

Asalin hoton,Reuters

A yau ɗin ne kuma yayin da Hamas ke sakin ‘yan Isra’ilar uku aka ga motocin safa-safa na Red Cross a wajen gidan yari na Ofer da ke yankin Gabar Yamma da Isra’ila ta mamaye, sun je domin ɗaukar fursunoni Falasɗinawa.

Hamas ta ce a duk mutum ɗaya da ta saki na Isra’ila za a saki Falasɗinawa 30 fursunoni daga gidan yarin Isra’ila.

A ranar 7 ga watan Oktoba na 2023 me Hamas ta kai wa Isra’ila wani harin bazata inda ta kashe kusan mutum 1,200 ta kuma yi garkuwa da 251 da ta kai Gaza. A cewar BBC.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...

Lakurawa sun kashe Mutane 15 a Sokoto

Wasu da ake zargin mambobin ƙungiyar Lakurawa ne sun...

Dan wasan Liverpool Diago Jota da Kaninsa sun mu a hadarin mota

Ɗan wasan ƙwallon ƙafar Liverpool kuma ɗan ƙasar Portugal,...

Mun shirya tunkarar APC a 2027 – ADC

A ranar Laraba ne manyan ƴan adawar siyasa suka...

Mun dagulawa Iran lisafi na tsawon shekaru biyu a nukiliyar ta – Amurka

Ma'aikatar tsaron Amurka ta ce bayannan leken asirinta ya...

INEC za ta fitar da sabbin ƙa’idojin duba sakamakon zaɓe

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya...
X whatsapp