fidelitybank

Ƴan Isra’ila da a ka fara saki sun koma gida

Date:

Hukumomin sojin Isra’ila sun tabbatar da cewa mata ukun nan da Hamas ta saki a cikin ‘yan ƙasar da ta yi garkuwa da su, yanzu sun koma Isra’ila daga Gaza.

A ɗazu ne Hamas ta danka matan ga ƙungiyar agaji ta duniya ta Red Cross, inda ‘yan Isra’ila da dama suka yi maraba tare da murna da sakin nasu, wanda suka kalla ta wani babban allon talabijin da aka girke a babban birnin Isra’ilar Tel Aviv.

Bayan an duba lafiyarsu da da farko daga nan za a tafi da su wani asibiti a kusa da babban birnin kafin kuma daga bisani a haɗa su da iyalansu.

An tabbatar da matan su ne waɗanda Hamas ta bayar da sunansu a waɗanda za ta fara saki – Doron Steinbrecher, da Romi Gonen da kuma Emily Damari.

Kakakin sojin Isra’ila Daniel Hagari a wani taron manema labarai ya ce a cikin wannan mako shida na farko za a rika sakin mutum uku ko hudu duk mako cikin wadanda Hamas ɗin ta yi garkuwa da su.

Wani jami’in Hamas ɗin ya sheda wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa a ranar Asabar za a yi musayar fursunonin ta gaba

Akwai ƙarin mutum 30 da Hamas ɗin za ta saki, rukuni-rukuni a cikin mako shida inda za a riƙa musayarsu da ɗaruruwan Falasɗinawa da ke gidajen yarin Isra’ila.

Motocin Red Cross

Asalin hoton,Reuters

A yau ɗin ne kuma yayin da Hamas ke sakin ‘yan Isra’ilar uku aka ga motocin safa-safa na Red Cross a wajen gidan yari na Ofer da ke yankin Gabar Yamma da Isra’ila ta mamaye, sun je domin ɗaukar fursunoni Falasɗinawa.

Hamas ta ce a duk mutum ɗaya da ta saki na Isra’ila za a saki Falasɗinawa 30 fursunoni daga gidan yarin Isra’ila.

A ranar 7 ga watan Oktoba na 2023 me Hamas ta kai wa Isra’ila wani harin bazata inda ta kashe kusan mutum 1,200 ta kuma yi garkuwa da 251 da ta kai Gaza. A cewar BBC.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp