Hukumomin sojin Isra’ila sun tabbatar da cewa mata ukun nan da Hamas ta saki a cikin ‘yan ƙasar da ta yi garkuwa da su, yanzu sun koma Isra’ila daga Gaza.
A ɗazu ne Hamas ta danka matan ga ƙungiyar agaji ta duniya ta Red Cross, inda ‘yan Isra’ila da dama suka yi maraba tare da murna da sakin nasu, wanda suka kalla ta wani babban allon talabijin da aka girke a babban birnin Isra’ilar Tel Aviv.
Bayan an duba lafiyarsu da da farko daga nan za a tafi da su wani asibiti a kusa da babban birnin kafin kuma daga bisani a haɗa su da iyalansu.
An tabbatar da matan su ne waɗanda Hamas ta bayar da sunansu a waɗanda za ta fara saki – Doron Steinbrecher, da Romi Gonen da kuma Emily Damari.
Kakakin sojin Isra’ila Daniel Hagari a wani taron manema labarai ya ce a cikin wannan mako shida na farko za a rika sakin mutum uku ko hudu duk mako cikin wadanda Hamas ɗin ta yi garkuwa da su.
Wani jami’in Hamas ɗin ya sheda wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa a ranar Asabar za a yi musayar fursunonin ta gaba
Akwai ƙarin mutum 30 da Hamas ɗin za ta saki, rukuni-rukuni a cikin mako shida inda za a riƙa musayarsu da ɗaruruwan Falasɗinawa da ke gidajen yarin Isra’ila.

Asalin hoton,Reuters
A yau ɗin ne kuma yayin da Hamas ke sakin ‘yan Isra’ilar uku aka ga motocin safa-safa na Red Cross a wajen gidan yari na Ofer da ke yankin Gabar Yamma da Isra’ila ta mamaye, sun je domin ɗaukar fursunoni Falasɗinawa.
Hamas ta ce a duk mutum ɗaya da ta saki na Isra’ila za a saki Falasɗinawa 30 fursunoni daga gidan yarin Isra’ila.
A ranar 7 ga watan Oktoba na 2023 me Hamas ta kai wa Isra’ila wani harin bazata inda ta kashe kusan mutum 1,200 ta kuma yi garkuwa da 251 da ta kai Gaza. A cewar BBC.