fidelitybank

Ƴan fashin daji sun kai hari Zariya sun kuma kashe mutum 4

Date:

 

Yan fashin daji sun kai hari kan unguwar Kofar Kona a Zariya ta Jihar Kaduna, inda su ka kashe mutum 4 su ka kuma  ji wa da dama rauni.
Majiyoyi sun baiyanawa jaridar DAILY NIGERIAN cewa ƴan ta’addan sun shiga unguwar a ranar Litinin da misalin ƙarfe 10 na dare, in da su ka riƙa harbi kan me-uwa-da-wabi.
An ce bayan harbe-harben, yan bindigar sun kaɗa wani garken shanu cikin jeji.
Jaridar ta ce wani mazaunin yankin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce mazauna unguwar sun yi ta kiran lambar ƴan sanda amma ba a amsa kiran nasu ba.
“mun yi ta kiran lambobin kar-ta-kwana na ƴan sanda amma ba amsa. Sai bayan ma yan bindigar sun ci karensu ba babbaka sannan yan sandan su ka zo.
“Wajen mutum 24 a ka garzaya da su asibitin Gambo Sawaba can a Ƙofar Gayan, in da 4 su ka rasu sakamakon harbin da a ka yi musu da yawa a jikunan su.
“Sun kuma tafi da garken shanu na wasu Fulani sabbin zuwa a yankin,” in ji shi.
Jaridar ta ƙara da cewa Kakakin Rundunar Ƴan Sanda ta Kaduna, Mohammed Jalige bai daga wayar da ta yi masa ba har zuwa lokacin da ta wallafa labarin.

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp