fidelitybank

Ƴan fashin daji sun kai hari Zariya sun kuma kashe mutum 4

Date:

 

Yan fashin daji sun kai hari kan unguwar Kofar Kona a Zariya ta Jihar Kaduna, inda su ka kashe mutum 4 su ka kuma  ji wa da dama rauni.
Majiyoyi sun baiyanawa jaridar DAILY NIGERIAN cewa ƴan ta’addan sun shiga unguwar a ranar Litinin da misalin ƙarfe 10 na dare, in da su ka riƙa harbi kan me-uwa-da-wabi.
An ce bayan harbe-harben, yan bindigar sun kaɗa wani garken shanu cikin jeji.
Jaridar ta ce wani mazaunin yankin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce mazauna unguwar sun yi ta kiran lambar ƴan sanda amma ba a amsa kiran nasu ba.
“mun yi ta kiran lambobin kar-ta-kwana na ƴan sanda amma ba amsa. Sai bayan ma yan bindigar sun ci karensu ba babbaka sannan yan sandan su ka zo.
“Wajen mutum 24 a ka garzaya da su asibitin Gambo Sawaba can a Ƙofar Gayan, in da 4 su ka rasu sakamakon harbin da a ka yi musu da yawa a jikunan su.
“Sun kuma tafi da garken shanu na wasu Fulani sabbin zuwa a yankin,” in ji shi.
Jaridar ta ƙara da cewa Kakakin Rundunar Ƴan Sanda ta Kaduna, Mohammed Jalige bai daga wayar da ta yi masa ba har zuwa lokacin da ta wallafa labarin.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp