fidelitybank

‘Ƴan APC za su karɓi kuɗin Tinubu kuma su ƙi zaɓar sa a 2023’

Date:

Babban Fasto na Cocin Divine Mercy, Olatobiloba Peters ya yi hasashen cewa ƴan jam’iya mai mulki ta APC za su ci kuɗin Bola Ahmed Tinubu ne kawai su kuma ko zabar sa.
Ya kuma gargaɗi Tinubun, mai neman tsayawa takarar shugaban ƙasa a 2023 da kada ya ci gaba da burinsa na zama shugaban ƙasa.
Fasto Peters ya ce ƴan jam’iyyar  APC, za su karɓi kuɗin Tinubu kawai kuma su ƙi kaɗa masa ƙuri’a.
Da yake zantawa da DAILY POST, limamin ya ce Ubangiji ne ya nuna masa cewa ‘yan APC za su yi amfani da kudin Tinubu su cicciɓa mataimakin shugaban kasa, Osinbajo ya zama shugaban kasa.
Tinubu, wanda ya sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasar a 2023, ya ce matakin wani buri ne a gare shi tsawon rayuwarsa.
Jagoran jam’iyyar APC na Ƙasa ya ce yana ci gaba da tuntuɓar masu ruwa da tsaki a kan matakin da ya ɗauka na maye gurbin Buhari a 2023.
Sai dai Fasto Peters ya ce Ubangiji ya halicci Tinubu ne domin ya kafa sarakuna ba wai shi ya zama ba.
Limamin ya bukaci tsohon gwamnan jihar Legas ɗin da kada ya barnatar da kudinsa a kan kudirinsa na shugaban kasa.
Sai dai ya yi gargadin cewa ‘yan Najeriya za su yi nadama idan har Tinubu ya tilasta wa kan sa mulki ta hanyar magudi.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp