fidelitybank

‘Ƴan APC za su karɓi kuɗin Tinubu kuma su ƙi zaɓar sa a 2023’

Date:

Babban Fasto na Cocin Divine Mercy, Olatobiloba Peters ya yi hasashen cewa ƴan jam’iya mai mulki ta APC za su ci kuɗin Bola Ahmed Tinubu ne kawai su kuma ko zabar sa.
Ya kuma gargaɗi Tinubun, mai neman tsayawa takarar shugaban ƙasa a 2023 da kada ya ci gaba da burinsa na zama shugaban ƙasa.
Fasto Peters ya ce ƴan jam’iyyar  APC, za su karɓi kuɗin Tinubu kawai kuma su ƙi kaɗa masa ƙuri’a.
Da yake zantawa da DAILY POST, limamin ya ce Ubangiji ne ya nuna masa cewa ‘yan APC za su yi amfani da kudin Tinubu su cicciɓa mataimakin shugaban kasa, Osinbajo ya zama shugaban kasa.
Tinubu, wanda ya sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasar a 2023, ya ce matakin wani buri ne a gare shi tsawon rayuwarsa.
Jagoran jam’iyyar APC na Ƙasa ya ce yana ci gaba da tuntuɓar masu ruwa da tsaki a kan matakin da ya ɗauka na maye gurbin Buhari a 2023.
Sai dai Fasto Peters ya ce Ubangiji ya halicci Tinubu ne domin ya kafa sarakuna ba wai shi ya zama ba.
Limamin ya bukaci tsohon gwamnan jihar Legas ɗin da kada ya barnatar da kudinsa a kan kudirinsa na shugaban kasa.
Sai dai ya yi gargadin cewa ‘yan Najeriya za su yi nadama idan har Tinubu ya tilasta wa kan sa mulki ta hanyar magudi.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp