Ƙungiyar gwamnoni ta ƙasa, ta yi Allah-wadai cikin kakkausar murya ga masu yunƙurin kafa gwamnatin riƙon ƙwarya, maimakon rantsar da shugabannin da aka zaɓa.
A wata sanarwa da ta fitar da sa hannun shugabanta, kuma gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, ƙungiyar ta ce za ta yi duk mai yiwuwa domin kare martabar dimokraɗiyyar Najeriya.
Haka kuma, ƙungiyar ta ce ba za ta goyi bayan duk wani abu da ya saɓa wa tsarin mulkin ƙasar ba.
Gwamnonin sun ce fitar da sanarwar cewa akwai masu yunƙurin kafa gwamnatin riƙo, ba tare da sanar sunayen masu maƙarƙashiyar ba, abu ne da zai iya haifar da ruɗani da fargaba a ƙasar.
Don haka gwamnonin suka yi kira ga hukumar tsaron farin kaya ta DSS, ta gaggauta kamawa tare da gurfanar da mutanen da ke da hannu a yunkurin kafa gwamnatin riƙo a gaban kotu.
Ƙungiyar ta kuma taya mambobinta da aka sake zaɓa a karo na biyu, murna.
Tana cewa duk da kura-kuran da aka samu a zaɓukan da suka gabata, ƙungiyar ta yi alƙawarin ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace don inganta dimokraɗiyya da harkokin zaɓen ƙasar.