fidelitybank

Ƙungiyar Gwamnoni ta yi tur da kafa gwamnatin riƙon ƙwarya a Najeriya

Date:

Ƙungiyar gwamnoni ta ƙasa, ta yi Allah-wadai cikin kakkausar murya ga masu yunƙurin kafa gwamnatin riƙon ƙwarya, maimakon rantsar da shugabannin da aka zaɓa.

A wata sanarwa da ta fitar da sa hannun shugabanta, kuma gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, ƙungiyar ta ce za ta yi duk mai yiwuwa domin kare martabar dimokraɗiyyar Najeriya.

Haka kuma, ƙungiyar ta ce ba za ta goyi bayan duk wani abu da ya saɓa wa tsarin mulkin ƙasar ba.

Gwamnonin sun ce fitar da sanarwar cewa akwai masu yunƙurin kafa gwamnatin riƙo, ba tare da sanar sunayen masu maƙarƙashiyar ba, abu ne da zai iya haifar da ruɗani da fargaba a ƙasar.

Don haka gwamnonin suka yi kira ga hukumar tsaron farin kaya ta DSS, ta gaggauta kamawa tare da gurfanar da mutanen da ke da hannu a yunkurin kafa gwamnatin riƙo a gaban kotu.

Ƙungiyar ta kuma taya mambobinta da aka sake zaɓa a karo na biyu, murna.

Tana cewa duk da kura-kuran da aka samu a zaɓukan da suka gabata, ƙungiyar ta yi alƙawarin ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace don inganta dimokraɗiyya da harkokin zaɓen ƙasar.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp