Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya baiwa jihar Zamfara tallafin kudi Naira miliyan 20, domin rage radadin da su ke ciki na harin ‘yan ta’adda.
Zulum wanda shi ne shugaban ƙuyngiyar gwamnonin, ya kai ziyarar ne a ranar Litinin a fadar gwamnatin jihar da ke Gusau.
Yayin ziyarar, gwamnan ya bai wa waɗanda tashin hankalin ya shafa tallafin Naira miliyan 20. Cikin waɗanda suka yi masa rakiya har da Sanata Ali Ndume, Shugaban Kwamatin Sojan Ƙasa a Majalisar Dattawa, da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Borno Abdullahi Musa Askira.
Da yake yi wa sarakunan gargajiyar yankin da kuma jami’an gwamnatin Zamfara jawabi, Gwamna Zulum ya ce“Kar ku karaya, irin ɓarnar da yaƙin Boko Haram ya haddasa a jihar mu, ba mu karaya ba”.