fidelitybank

Zub da Jini: Zuwa ga shugabannin hukumomin tsaro – Arewa Media Writers

Date:

Ƙungiyar Marubutan Arewa “Arewa Media Writers” ta aikewa shugabannin hukumomin tsaron Najeriya Saƙonnin halin da Al’ummar Arewa ke ciki.

Kungiyar ta bukaci gwamnatin Najeriya da ta ɗauki matakin gaggawa, donmi kawo ƙarshen matsalolin rashin tsaron da ya yi muni a yankin Arewa.

Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Comr Abba Sani Pantami ne ya aikewa manema labarai, inda kungiyar ta turawa shugabannin hukumomin tsaron Najeriya sakonnin halin da al’ummar Arewa suke ciki na taɓarɓarewar tsaro, musamman a ƴan kwanakin nan.

Haka zalika ƙungiyar ta buƙaci gwamnatin ƙasar da ta tashi tsaye kan taɓarɓarewar tsaron da yayi muni a yankin Arewa dama ƙasar Najeriya baki ɗaya.

Ƙungiyar ta bayyana hakan ne, a cikin takaddun ƙorafi da ta turawa hukumomin tsaron mai ɗauke da sa hannun shugaban ƙungiyar na ƙasa Comr Abba Sani Pantami, inda ƙungiyar ta bayana irin takaici da jimamin halin da al’ummar Arewa suke ciki, na rashin zaman lafiya, rashin kwanciyar hankali, ga kuma talauci da tsadar Rayuwa da al’ummar yankin suke ciki.

Ga wani sashi na saƙon da ƙungiyar ta turawa hukumomin tsaron;

“Mun yi imanin cewa kuna da kayan aiki don kawo ƙarshen waɗannan matsalolin, amma abin takaici ba mu ga wani sakamako mai kyau ba har yau. Domin magance waɗannan matsalolin, dole ne gwamnati ta ƙara yawan jami’an tsaro akan jami’an da muke da su, tare da samar da guraben ayyukan yi da dama ga matasanmu. Akwai buƙatar matasanmu su kasance masu ilmi musamman waɗanda ke zaune a yankin da babu makarantu, asibitoci, ruwa, hanyoyi da sauransu. A ƙarshe, muna buƙatar ɗaukar matakin gaggawa don kawo ƙarshen matsalolin”.

Sanarwar ta ci gaba da cewa,”Muna son zaman lafiya da adalci wanda zai iya haifar da ingantacciyar rayuwa ta al’ummarmu a dukkan jihohin Arewa da Najeriya baki ɗaya. Arewa Media Writers” za ta ci gaba da ƙoƙarin kawar da duk wasu labaran ƙarya da ka iya kawo matsala a wurin yaƙi da ƴan ta’addan tare da cigaba da wayarwa al’umma kai domin samun ci gaba da haɗin kai da cikakken haɗin kan Al’ummar mu. Mungode da fahimtar sakonmu”. A cewar Arewa Media Writers.

nigeria news today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp