fidelitybank

Zub da Jini: Zuwa ga shugabannin hukumomin tsaro – Arewa Media Writers

Date:

Ƙungiyar Marubutan Arewa “Arewa Media Writers” ta aikewa shugabannin hukumomin tsaron Najeriya Saƙonnin halin da Al’ummar Arewa ke ciki.

Kungiyar ta bukaci gwamnatin Najeriya da ta ɗauki matakin gaggawa, donmi kawo ƙarshen matsalolin rashin tsaron da ya yi muni a yankin Arewa.

Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Comr Abba Sani Pantami ne ya aikewa manema labarai, inda kungiyar ta turawa shugabannin hukumomin tsaron Najeriya sakonnin halin da al’ummar Arewa suke ciki na taɓarɓarewar tsaro, musamman a ƴan kwanakin nan.

Haka zalika ƙungiyar ta buƙaci gwamnatin ƙasar da ta tashi tsaye kan taɓarɓarewar tsaron da yayi muni a yankin Arewa dama ƙasar Najeriya baki ɗaya.

Ƙungiyar ta bayyana hakan ne, a cikin takaddun ƙorafi da ta turawa hukumomin tsaron mai ɗauke da sa hannun shugaban ƙungiyar na ƙasa Comr Abba Sani Pantami, inda ƙungiyar ta bayana irin takaici da jimamin halin da al’ummar Arewa suke ciki, na rashin zaman lafiya, rashin kwanciyar hankali, ga kuma talauci da tsadar Rayuwa da al’ummar yankin suke ciki.

Ga wani sashi na saƙon da ƙungiyar ta turawa hukumomin tsaron;

“Mun yi imanin cewa kuna da kayan aiki don kawo ƙarshen waɗannan matsalolin, amma abin takaici ba mu ga wani sakamako mai kyau ba har yau. Domin magance waɗannan matsalolin, dole ne gwamnati ta ƙara yawan jami’an tsaro akan jami’an da muke da su, tare da samar da guraben ayyukan yi da dama ga matasanmu. Akwai buƙatar matasanmu su kasance masu ilmi musamman waɗanda ke zaune a yankin da babu makarantu, asibitoci, ruwa, hanyoyi da sauransu. A ƙarshe, muna buƙatar ɗaukar matakin gaggawa don kawo ƙarshen matsalolin”.

Sanarwar ta ci gaba da cewa,”Muna son zaman lafiya da adalci wanda zai iya haifar da ingantacciyar rayuwa ta al’ummarmu a dukkan jihohin Arewa da Najeriya baki ɗaya. Arewa Media Writers” za ta ci gaba da ƙoƙarin kawar da duk wasu labaran ƙarya da ka iya kawo matsala a wurin yaƙi da ƴan ta’addan tare da cigaba da wayarwa al’umma kai domin samun ci gaba da haɗin kai da cikakken haɗin kan Al’ummar mu. Mungode da fahimtar sakonmu”. A cewar Arewa Media Writers.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp