fidelitybank

Ziyarar Aiki: Buhari ya tafi kasar Turkiyya

Date:

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari zai bar Abuja zuwa birnin Santanbul na ƙasar Turkiyya, domin halartar taron haɗin gwiwa tsakanin Turkiyya da Afirka karo na uku wanda shugaba Recep Tayyip Erdogan na Turkiyya zai karɓi baƙwancin sa.

Mai taimaka wa shugaba Buhari kan harkokin yaɗa labarai Malam Garba Shehu, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar da safiyar ranar Alhamis a birnin tarayya Abuja.

A cewar masu shirya taron, taken sa shi ne ” Samar da ingantacciyar hadin gwiwa domin samun ci gaba da ƙaruwar arziki yayin da kuma yake da mauduin yin nazari kan haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen Afirka da Turkiyya tun bayan taron ƙarshe na shekarar 2014 da aka gudanar.”

“Taron hadin gwiwa tsakanin Turkiyya da Afirka na ukun dai yana zuwa ne a daidai bayan da shugaba Erdogan ya kawo ziyarar aiki Najeriya a kwanakin baya, inda aka sanya hannu kan yarjejeniyoyi da dama a fannonin makamashi harkokin tsaro sai haƙar maadinai da maadinan ruwa duk domin ƙarfafa alaƙar da ke tsakanin ƙasashen biyu.”

“Shugaban na Turkiyya a ziyarar da ya kawo Najeriya, ya tabbatar da aniyarsa ta gaggauta faɗaɗa harkokin kasuwancin da ke tsakanin kasashen biyu zuwa dala biliyan biyar, kuma tawagar Najeriya za ta yi amfani da damar taron da za a yi a Istanbul domin inganta haɗin gwiwa da sauran abokan hulɗar kasuwanci, ƙarin damar kasuwanci da zuba jari a kasar.”

Sanarwar ta kuma ce, a na sa ran taron zai samar da ƙa’idoji da alƙibilar haɗin gwiwa da ƙasashen Afirka a cikin shekaru biyar masu zuwa.

Shugaba Buhari zai samu rakiyar uwargidansa Aisha da ministocin da suka haɗa da na harkokin waje Geoffrey Onyeama da na Tsaro Manjo Janar Bashir Magashi mai ritaya da Ministan babban birnin tarayya Abuja Mohammed Bello da na Lafiya Osagie Ehanire sai na Noma Mohammed Abubakar da na Masana’antu Ciniki da Zuba Jari Adeniyi Adebayo.

Sauran sun haɗa da, mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya da babban Daraktan hukumar leƙen asiri ta ƙasa Ambasada Ahmed Rufa’i.

latest news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp