fidelitybank

Ziyarar Aiki: Buhari ya tafi kasar Turkiyya

Date:

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari zai bar Abuja zuwa birnin Santanbul na ƙasar Turkiyya, domin halartar taron haɗin gwiwa tsakanin Turkiyya da Afirka karo na uku wanda shugaba Recep Tayyip Erdogan na Turkiyya zai karɓi baƙwancin sa.

Mai taimaka wa shugaba Buhari kan harkokin yaɗa labarai Malam Garba Shehu, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar da safiyar ranar Alhamis a birnin tarayya Abuja.

A cewar masu shirya taron, taken sa shi ne ” Samar da ingantacciyar hadin gwiwa domin samun ci gaba da ƙaruwar arziki yayin da kuma yake da mauduin yin nazari kan haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen Afirka da Turkiyya tun bayan taron ƙarshe na shekarar 2014 da aka gudanar.”

“Taron hadin gwiwa tsakanin Turkiyya da Afirka na ukun dai yana zuwa ne a daidai bayan da shugaba Erdogan ya kawo ziyarar aiki Najeriya a kwanakin baya, inda aka sanya hannu kan yarjejeniyoyi da dama a fannonin makamashi harkokin tsaro sai haƙar maadinai da maadinan ruwa duk domin ƙarfafa alaƙar da ke tsakanin ƙasashen biyu.”

“Shugaban na Turkiyya a ziyarar da ya kawo Najeriya, ya tabbatar da aniyarsa ta gaggauta faɗaɗa harkokin kasuwancin da ke tsakanin kasashen biyu zuwa dala biliyan biyar, kuma tawagar Najeriya za ta yi amfani da damar taron da za a yi a Istanbul domin inganta haɗin gwiwa da sauran abokan hulɗar kasuwanci, ƙarin damar kasuwanci da zuba jari a kasar.”

Sanarwar ta kuma ce, a na sa ran taron zai samar da ƙa’idoji da alƙibilar haɗin gwiwa da ƙasashen Afirka a cikin shekaru biyar masu zuwa.

Shugaba Buhari zai samu rakiyar uwargidansa Aisha da ministocin da suka haɗa da na harkokin waje Geoffrey Onyeama da na Tsaro Manjo Janar Bashir Magashi mai ritaya da Ministan babban birnin tarayya Abuja Mohammed Bello da na Lafiya Osagie Ehanire sai na Noma Mohammed Abubakar da na Masana’antu Ciniki da Zuba Jari Adeniyi Adebayo.

Sauran sun haɗa da, mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya da babban Daraktan hukumar leƙen asiri ta ƙasa Ambasada Ahmed Rufa’i.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp