fidelitybank

Zargin Almundahana: Kotu ta bada belin Shugaban Ƙaramar Hukumar Fagge, Shehi

Date:

Babbar Kotun jiha mai zamanta a Mila road ta bada belin Shugaban Ƙaramar Hukumar Fagge, Ibrahim Abdullahi Shehi.

A yau Laraba ne dai Hukumar yaƙi da Cin-hanci mai zaman kanta, ICPC ta gurfanar da Shehi kan laifuka huɗu da suka shafi almundahana a kan kuɗaɗen harajin da ƙaramar hukumar ke tarawa.

Laifukan sun haɗa da yin amfani da ikon mulki ya fifita wasu ma’aikata a kan wasu, baiwa wasu masu karɓar haraji kaso 20 na kuɗin da a ka tara har karo huɗu da kuma sauran laifuka sa su ka shafi almundahana.

Bayan an karanta masa laifukansa, sai Shehi ya musa.

Daga bisani alƙalin kotun, Jamilu Sulaiman ya bada belin shugaban ƙaramar hukumar amma sai ya bada Naira dubu ɗari biyar.

Alƙalin ya ce ya bada belin Shehin ne sabo da shi mai mulki ne.

Ya ɗage zaman sai ranar 17 ga Janairu, 2022 domin sauraron ƙara.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp