Shugaban ‘yan sandan Japan ya ce, zai yi murabus daga mukaminsa, saboda kisan da aka yi wa tsohon firaiministan kasar Shinzo Abe.
Itaru Nakamura, shugaban hukumar da ke kula da ayyukan, ‘yan sandan kasar ya ce, yana so ya dauki alhakin harbin da aka yi wa tsohon firaiministan kasar a ranar 8 ga watan Yuli.
Binciken da aka yi ya gano cewa, akwai sakaci sosai a kan yadda aka ba wa Shinzo Abe, kariya a lokacin da lamarin ya afku.
An harbi mr Abe ne a yayin da ya ke jawabi a wani wajen gangamin yakin neman zabe a birnin Nara.
Wani mutum dan shekarar 41 ne ya harbi mr Abe a wuya abin da ya yi sanadin mutuwarsa. In ji BBC.