fidelitybank

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Date:

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya bayyana cewa wani matashi Yusuf ya rasa ransa a kamfanin Mamuda Group da ke Challawa, Jihar Kano, bayan da aka ce wani supervisor ya daɓa masa wuka.

Wasu rahotonnin dai daga Social Media sun ce an sallami matashin a aiki shi ne ya je karbar kudin sallama a nan supervisor din ya caka masa wuka.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da dangin mamacin ke kira ga hukumomi da su gudanar da cikakken bincike, tare da neman a tabbatar da adalci.

To amma a hirar da mahaifiyar marigayin ta yi da tashar Freedom Radio da ke Kano ta ce wanda ya caka masa wukar dama can suna da sabani tsawon lokaci.

Me kamfanin Mamuda Group ke cewa a kai?

Jamiʼin yada labaran kamfanin Bashir Alhasan Indabawa ya karyata wannan zargin cewa a kamfanin aka kashe matashi.

Ya ce, hatsaniyar ta faru ne tsakanin wasu ma’aikata biyu a wajen harabar kamfanin, kuma wanda ya caka wukar ba supervisor ba ne, dukkansu kananan maʼaikata ne a kamfanin.

Ya ƙara da cewa, suna da shaida cewa maʼaikatan su 2 sun bada uzri don fita daga kamfanin a wannan lokacin, kuma suna da bidiyo da kamfanin ya nada na duk abin da ya faru a harabarsa.

Ya ce, kuma duk da hakan ma’aikatan kamfanin ne suka kai wanda aka jikkata asibiti tare da hadin gwiwar ’yan sanda, kafin daga bisani ya rasu.

Yanzu haka dai ana ci gaba da jiran karin bayani daga rundunar ’yan sanda da sauran hukumomi, yayin da al’umma ke ci gaba da bayyana ra’ayoyi kan lamarin.

Warning
Warning
Warning
Warning

Warning.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...

Da Ɗumi-Ɗumi: Kashim Shettima zai rako gawar Muhammadu Buhari zuwa Najeriya

Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya rasu. Ya rasu ne...

Ina Tinubu ya ke ya ɓata ba bayani – ADC

Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC, ta soki Shugaba,...

Koriya ta Arewa za ta ba Rasha ƙarin sojoji domin yaƙin Ukraine

Shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya yi...

Jam’iyyar ADC alheri ce ga siyasar Najeriya – Femi Gbajabiamila

Shugaban ma'aikata na fadar gwamnatin Najeriya, Femi Gbajabiamila ya...

Tinubu na yunkurin tauye hakkin ma’aikata – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a Najeriya, Atiku Abubakar, ya...

Trump ya lafta wa ƙasashen Tarayyar Turai da Mexico harajin kashi 30

Shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa ƙasashen ƙungiyar...

INEC ta ce za ta buɗe shafin intanet domin rajistar sababbin jam’iyyu

Huhukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, ta ce nan...

EFCC na neman Rabi’u Auwalu Tijjani ruwa a jallo a Kano

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin...

An gano musabbabin hatsarin jirgin saman Indiya

Masu bincike sun bayyana sakamako na farko-farko game da...

Amurka ta haramta wa shugaban kasar Cuba shiga kasar

Amurka a karon farko ta ƙaƙaba takunkumi kan shugaban...

An kashe mutum 6,800 tare da sace 5,402 a 2025 Najeriya – Rahoto

Alƙaluma na nuna cewa an kashe mutum dubu shida...
X whatsapp