Jagoran jamâiyyar APC na kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ce tabbas zai tsaya takarar shugaban kasa a zaben 2023 mai zuwa.
Tsohon gwamnan na Legas ya shaida wa manema labarai bayan ganawarsa da shugaban kasa, Muhammadu Buhari, cewa ya sanar da shugaban aniyarsa ta tsayawa takara a ganawar da su ka yi da safiyar ranar Litinin a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Yayin da ya ke zantawa da âyan manema labarai a fadar gwamnati, Tinubu ya ce, burinsa na zama shugaban Najeriya ne na tsawon rayuwarsa.
Ya ce,âSa nasarorin da na samu a matsayin da na yin a gwamnan Legas, ina da karfin gwiwa na iya mulkin Najeriyaâ.
Tinubu ya kuma ka amsa tambayar cewa, yiwuwar takaran tikitin jamâiyyar APC tsakanin sa da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo wanda kuma a ke kyautata zaton ya na da shaâawar tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.