fidelitybank

Zan rattaba hannu a kan kashe Abdulmalik – Ganduje

Date:

Gwamna jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya ce, ba zai bata lokaci ba, wajen sanya hannu kan aiwatar da hukuncin kisa ga wadanda suka yi kisan gillar da aka yi wa yarinya ‘yar shekara biyar Hanifa Abubakar.

Ganduje ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar jaje ga iyalan yarinyar da aka kashe a Dakata Kawaji tare da mataimakinsa, Dr Nasiru Yusuf Gawuna da shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin jihar, Labaran Abdul Madari da sauran manyan jami’an gwamnati a ranar Litinin.

Ya ce,“Zan bi dokar da kundin tsarin mulki ya tanadar a matsayina na gwamnan Kano na amincewa da hukuncin kisa a yanayin da kotu ta yanke kan masu laifin. Muna da kwakkwaran tabbaci daga kotun da ke tafiyar da lamarin cewa, za a yi adalci, ba za mu yi jinkiri ba,” in ji shi.

Da yake tabbatar da cewa, “Duk wanda aka samu da wannan danyen aiki, shima zai fuskanci kisa ba tare da bata lokaci ba. A matsayinmu na gwamnati, mun riga mun fara aikin.”

“Tsarin mulkinmu ya tanadi cewa, idan aka yanke hukuncin kisa, ikon mulki ne na gwamna ya amince a aiwatar da hukuncin kisa. Ina tabbatar muku da haka, ba zan bata koda dakika daya ba. A gaggauta gudanar da shari’a, gwamnati za ta kula da iyalan marigayiyarmu Hanifa mai albarka.” A cewar Ganduje.

Ganduje ya kuma ce gwamnatinsa za ta yi wani abu a kan makarantun da bala’in ya shafa.

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp