fidelitybank

Zan rattaba hannu a kan kashe Abdulmalik – Ganduje

Date:

Gwamna jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya ce, ba zai bata lokaci ba, wajen sanya hannu kan aiwatar da hukuncin kisa ga wadanda suka yi kisan gillar da aka yi wa yarinya ‘yar shekara biyar Hanifa Abubakar.

Ganduje ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar jaje ga iyalan yarinyar da aka kashe a Dakata Kawaji tare da mataimakinsa, Dr Nasiru Yusuf Gawuna da shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin jihar, Labaran Abdul Madari da sauran manyan jami’an gwamnati a ranar Litinin.

Ya ce,“Zan bi dokar da kundin tsarin mulki ya tanadar a matsayina na gwamnan Kano na amincewa da hukuncin kisa a yanayin da kotu ta yanke kan masu laifin. Muna da kwakkwaran tabbaci daga kotun da ke tafiyar da lamarin cewa, za a yi adalci, ba za mu yi jinkiri ba,” in ji shi.

Da yake tabbatar da cewa, “Duk wanda aka samu da wannan danyen aiki, shima zai fuskanci kisa ba tare da bata lokaci ba. A matsayinmu na gwamnati, mun riga mun fara aikin.”

“Tsarin mulkinmu ya tanadi cewa, idan aka yanke hukuncin kisa, ikon mulki ne na gwamna ya amince a aiwatar da hukuncin kisa. Ina tabbatar muku da haka, ba zan bata koda dakika daya ba. A gaggauta gudanar da shari’a, gwamnati za ta kula da iyalan marigayiyarmu Hanifa mai albarka.” A cewar Ganduje.

Ganduje ya kuma ce gwamnatinsa za ta yi wani abu a kan makarantun da bala’in ya shafa.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp