fidelitybank

Zan rattaba hannu a kan kashe Abdulmalik – Ganduje

Date:

Gwamna jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya ce, ba zai bata lokaci ba, wajen sanya hannu kan aiwatar da hukuncin kisa ga wadanda suka yi kisan gillar da aka yi wa yarinya ‘yar shekara biyar Hanifa Abubakar.

Ganduje ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar jaje ga iyalan yarinyar da aka kashe a Dakata Kawaji tare da mataimakinsa, Dr Nasiru Yusuf Gawuna da shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin jihar, Labaran Abdul Madari da sauran manyan jami’an gwamnati a ranar Litinin.

Ya ce,“Zan bi dokar da kundin tsarin mulki ya tanadar a matsayina na gwamnan Kano na amincewa da hukuncin kisa a yanayin da kotu ta yanke kan masu laifin. Muna da kwakkwaran tabbaci daga kotun da ke tafiyar da lamarin cewa, za a yi adalci, ba za mu yi jinkiri ba,” in ji shi.

Da yake tabbatar da cewa, “Duk wanda aka samu da wannan danyen aiki, shima zai fuskanci kisa ba tare da bata lokaci ba. A matsayinmu na gwamnati, mun riga mun fara aikin.”

“Tsarin mulkinmu ya tanadi cewa, idan aka yanke hukuncin kisa, ikon mulki ne na gwamna ya amince a aiwatar da hukuncin kisa. Ina tabbatar muku da haka, ba zan bata koda dakika daya ba. A gaggauta gudanar da shari’a, gwamnati za ta kula da iyalan marigayiyarmu Hanifa mai albarka.” A cewar Ganduje.

Ganduje ya kuma ce gwamnatinsa za ta yi wani abu a kan makarantun da bala’in ya shafa.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp