Wata gobara ta kone ofishin rigakafi na kasa (NPI) dake karamar hukumar Rogo a jihar Kano.
A wani jawabi a lokacin da yake karbar wata tawaga mai karfi daga hukumar kula da lafiya a matakin farko shugaban karamar hukumar Rogo, Alhaji Mubarak Bashir Fulatan, wanda mataimakinsa shugaban karamar hukumar, Alhaji Sabiu Surajo Rogo ya wakilta ya bayyana cewa gobara har yanzu ba a san musabbabin tashin ta ba, wadda ta lalata wuraren adana alluran rigakafi da muhimman takardu da kuma ginin baki.
Cikin Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na ma’aikatar lafiya a matakin farko ta Jihar Kano, maikudi Muhammad Marafa ya rabawa manema labarai, ya ce tun da farko a nasa jawabin, babban sakataren hukumar kula da lafiya matakin farko ta jiha, Dr. Tijjani Hussain wanda ya samu wakilcin manajan shirin SERICC Dr. Habib Tijjani Gwarzo, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici matuka.
Ya kuma bayyana cewa gobarar ta kawo koma baya ga ayyukan rigakafi na yau da kullum a yankin, za a dauki dukkan matakan da suka dace, domin samar da matakan gaggawa bayan tattara rahoton da kwamitin ya tantance.