fidelitybank

Zamu dawo da ma’aikatan jinya da likitoci masu aiki a waje – Gwamnati

Date:

Ministan Lafiya dakta Osagie Ehanire, ya ce, gwamnatin tarayya na wani shiri domin maido da likitoci da ma’aikatan jinya ‘yan asalin Najeriya da ke aiki a ƙasashen waje, tare da maida su aiki a jami’o’i da asibitocin ƙasar nan.

Yayin da yake jawabi a wajen gabatar da nasarorin da ma’aikatun gwamnatin tarayya suka samu ƙarƙashin wannan gwamnati ranar Talata a Abuja babban birnin ƙasar, ministan ya ce ya fahimci yadda ƙwararrun likitoci ke bariin ƙasar.

Ministan ya ce da yawa daga cikin likitoci da ma’aikatan jinya suna ganin kamar ba a biyansu ladan aikin da suke yi kamar yadda ya kamata.

Mista Ehanire ya ce gwamnatin tarayya na ƙoƙarin magance matsalar ta hanyar inganta yanayin aikin likitocin.

Ya ƙara da cewa matsalar ƙarancin likitoci matsala ce da ta shafi duniya baki-ɗaya, ba Najeriya kaɗai ba.

Ya ci gaba da cewa ”A wani zama da muka yi da ministan lafiya na ƙasar Gambiya ya yi min ƙorafi game da yadda likitoci ke barin ƙasar”.

”Sannan kuma na zanta da hukumomin Birtaniya waɗanda suma suka sanar da ni cewa mafi yawan likitocin ƙasar na tafiya Canada da New Zealand inda ake biyan albashi mai gwaɓi, dan haka suke buƙatar ƙarain likitoci a ƙasarsu, sannan haka lamarin yake a Masar da Turkiyya”.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...

Na ki marawa Atiku baya ne saboda juyin yankin Kudu ne – Wike

Ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike, a wata...

An saki sakamakon jarabawar WASSCE

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma ta fitar da...

Sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa wajen karbar abinci

Rahotanni daga Gaza na cewa sojojin Isra'ila sun sake...

Ambaliya ya shanye jihohin Bauchi da Filato da kuma Neja

Ambaliya ta cinye gonaki da gidaje da makarantu da...

Najeriya ta lashe gasar kwallon kwandon Afrika

Tawagar ƴan wasan kwando na matan Najeriya ta lashe...

Obi ba zai iya lashe zabe a yankin Arewa ba – Keyamo

Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya ce ɗaya...

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...
X whatsapp