Majalisar wakilai ta tarayya ta gayyaci shugaban hukumar zabe ta kasa, Farfesa Mahmud Yakubu ya je gabanta ya yi bayani a kan kudin da za a kashe na zaben fidda gwani na ƴar tinke, wanda dama ke cikin sabuwar dokar zaben da ƴan majalisar su ka zartar kwanan nan.
Batun zaben fid da gwanin ya janyo ce-ce-kuce a Najeriya, kasancewar gwamnonin jihohi suna adawa da tsarin ƴar tinken, yayin da ƴan majalisa ke cewa shi ne ya fi dacewa.
BBC ta rawaito, Ƴan majalisar wakilan sun amince da aika wa shugaban hukumar zaben kasar, Farfesa Mahmud Yakubu goron gayyata ne, bayan dan majalisa daga jihar Kogi, Leke Abejide ya gabatar da kudurin a jerin batutuwa masu bukatar kulawar gaggawa.
Ƴan majalisar sun ce su na jin ana cewa zaben fid da gwanin kadai idan jam’iyyun siyasar kasar za su yi shi kai-tsaye, wanda zai lashe fiye da Naira biliyan 500.