Gidauniyar Panacea Foundation mai zaman kanta a Kano, ta ce za ta dasa bishiyu 100,000 a makarantun Kano da al’umma a shekarar 2022.
Wanda ya kafa kungiyar, Dahir Hashim, ya zanta da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ranar Talata a Kano.
Hashim ya ce, an yi aikin ne da nufin dakile matsalar zafi a Kano.
“Za mu mai da hankali kan shuka a makarantu ta yadda dalibai za su samu damar sanin kansu da dashen itatuwa da kuma kula da su,” in ji shi.
A cewar Hashim, manufar dashen bishiyar ita ce yin tasiri ga dimbin sake koren garin Kano.
“A shekarar 2021, mun dasa bishiyoyi sama da 10,000 a makarantu da al’ummomi daban-daban a cikin kananan hukumomin Kano.
“A wannan lokacin, mun shirya gangamin wayar da kan jama’a, domin wayar da kan muhalli tsakanin yaran makaranta, al’ummomi, da ofisoshin gwamnati,” in ji shi.
Hashim ya ce, gidauniyar ta kuma horas da kungiyoyi masu zaman kansu kan yadda za su kula da bishiyun da kuma yadda za a rika samar musu da taki na gida.
Ya ce gidauniyar ta na da ‘yan agaji da s uka yi aiki a matsayin masu kula da kowace karamar hukuma a fadin jihar.
Hashim ya ce “Muna yin wadannan duka ne domin ganin an kula da itatuwan da mu ka dasa sosai kuma dukkansu za su tsiro domin amfanin al’umma.”
Ya kara da cewa aikin shine domin inganta rayuwar al’umma gaba daya a Kano.
Hashim ya roki goyon bayan jama’a wajen ganin Kano ta zama koraye, domin kare birnin daga sauyin yanayi.