fidelitybank

Za mu mamaye Kano da bishiyu – Gidauniyar Panacea Foundation

Date:

Gidauniyar Panacea Foundation mai zaman kanta a Kano, ta ce za ta dasa bishiyu 100,000 a makarantun Kano da al’umma a shekarar 2022.

Wanda ya kafa kungiyar, Dahir Hashim, ya zanta da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ranar Talata a Kano.

Hashim ya ce, an yi aikin ne da nufin dakile matsalar zafi a Kano.

“Za mu mai da hankali kan shuka a makarantu ta yadda dalibai za su samu damar sanin kansu da dashen itatuwa da kuma kula da su,” in ji shi.

A cewar Hashim, manufar dashen bishiyar ita ce yin tasiri ga dimbin sake koren garin Kano.

“A shekarar 2021, mun dasa bishiyoyi sama da 10,000 a makarantu da al’ummomi daban-daban a cikin kananan hukumomin Kano.

“A wannan lokacin, mun shirya gangamin wayar da kan jama’a, domin wayar da kan muhalli tsakanin yaran makaranta, al’ummomi, da ofisoshin gwamnati,” in ji shi.

Hashim ya ce, gidauniyar ta kuma horas da kungiyoyi masu zaman kansu kan yadda za su kula da bishiyun da kuma yadda za a rika samar musu da taki na gida.

Ya ce gidauniyar ta na da ‘yan agaji da s uka yi aiki a matsayin masu kula da kowace karamar hukuma a fadin jihar.

Hashim ya ce “Muna yin wadannan duka ne domin ganin an kula da itatuwan da mu ka dasa sosai kuma dukkansu za su tsiro domin amfanin al’umma.”

Ya kara da cewa aikin shine domin inganta rayuwar al’umma gaba daya a Kano.

Hashim ya roki goyon bayan jama’a wajen ganin Kano ta zama koraye, domin kare birnin daga sauyin yanayi.

 

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaÉ—i masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga FalasÉ—inawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen É—an gwagwarmayar nan kuma É—an jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp