Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki don hana sake faruwar kisan mutane a jihar bayan kisan wasu ƴan asalin jihar Kaduna a ƙaramar hukumar Mangu da ke jihar.
A makon jiya ne dai aka kashe wasu matafiya 12 ƴan Zaria, da ba su ji ba su gani ba, wani abu da ya janyo Allah-wadai daga ɓangarori daban-daban.
Joyce Ramnav, ita ce kwamishiniyar watsa labarai a jihar ta Filato, ta bayyanawa BBC cewa burinsu shi ne su nuna wa duniya cewa Filato jiha ce mai son zaman lafiya, mai maraba da mutane.
Ta ce, “jami’an tsaron sun kama mutum 22, kuma idan allah ya yarda gwamnati za ta ɗauki matakin domin a tabbatar an hukunta waɗannan mutane.”
Ta ce yanzu gwamnati na jiran sakamakon bincike ne da ƴansandan jihar ke gabatarwa, “kafin mu san matakin da za mu ɗauka na gaba.”