fidelitybank

Za mu ƙwace lasisin masu rage litar fetur – NMDPRA

Date:

Hukumar da ke sa ido kan harkokin man fetur ta Najeriya (NMDPRA) ta ce, za ta kakabawa gidajen mai da ke sauya fanfunan mai.

Farouk Ahmed, Shugaban Hukumar NMDPRA ne ya bayyana haka a wata ganawa da ya yi da kwamishinonin Hukumar tattara kudaden shiga da kasafi (RMAFC) ranar Juma’a a Abuja.

Ahmed ya ce gidajen man da aka kama suna rarraba mai tare da gyaran famfunan mai za su fuskanci tsauraran takunkumi, da suka hada da soke lasisin aiki, dakatarwa daga aiki, ko kuma rufewa, ya danganta da girman laifin.

A cewarsa, gyaran fanfunan mai da masu gidajen mai ke yi, babban abin damuwa ne ga hukumomin kula da mai da kuma gwamnatin tarayya.

“Abin da muke yi a yanzu shi ne, muna da wasu ma’aikatanmu da ke zagayawa domin yin bincike a kan wasu gidajen mai. Idan ka shiga tasha ka fita, ba za ka san ko an yaudare ka ba sai ka yi awo.

“Wani lokaci muna yin awo na jiki inda muke zuwa wasu tashoshi mu sayi lita daya mu duba wannan muhallin mu ga ko da gaske wannan lita daya ce. Daga nan za mu san ko sun yi wa famfo ne ko a’a,” inji shi.

Shugaban NMDPRA ya ce hukumar za ta ci gaba da hada kai da RMAFC domin samar da karin kudaden shiga ga hukumar.

“Mun fara aikin, amma wannan hadin gwiwa ne kawai a kan bangarorin da za mu iya inganta samar da kudaden shiga ga tarayya. Akwai fannoni guda biyu da ya kamata mu duba, ko dai don samar da kudaden shiga ko rage kashe kudi,” inji shi.

Ya yi kira ga ‘yan kasa da su saka hannun jari a bangaren tattalin arziki mai tsaka-tsaki, yana mai cewa: “Misali, idan kuna son gina masana’antar iskar gas, ku zo wurinmu; za mu ba ku jagorori da manufofi, kuma za ku zo ku saka hannun jari. Yankin da kake son saka hannun jari zai ƙayyade farashin zuba jari; da damar zuba jari a can.”

Shugaban RMAFC, Mista Bello Shehu, ya ce makasudin kulla alaka tsakanin kungiyoyin biyu shi ne karfafa hadin gwiwarsu.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp