Hukumomi a jihar Darfur ta Arewacin kasar Sudan sun sanar da kafa dokar hana fita da daddare a ranar Laraba bayan da wasu kungiyoyi dauke da makamai su ka yi awon gaba da wani rumbun adana kayan abinci na Majalisar Dinkin Duniya da kayayyakin da wata tsohuwar tawagar wanzar da zaman lafiya ke amfani da ita.
A cewar rahotannin farko na Majalisar Dinkin Duniya da ta fitar cewa, rumbun ajiyar kayayyaki da ke El Fasher da wasu kungiyoyi dauke da makamai su ka wawashe a yammacin ranar Talatar da ta gabata, na kunshe da ton 1,900 na abinci da a ka tanada, domin dubban daruruwan mutane a yankin.
Rikici da kone-kone ya lalata shagunan, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na SUNA ya ruwaito. A ranar Laraba, an ji karar harbe-harbe a kusa da wurin ajiyar rumbin abincin, kamar yadda wani mazaunin garin ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.
“Daya daga cikin mutane uku a Sudan na bukatar agajin jin kai. Irin wannan harin ya na matukar kawo cikas ga iya kai ga mutanen da suka fi bukata,” inji jami’ar kula da ayyukan jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya Khardiata Lo N’diaye.