A daidai ƙarfe 9:15 agogon GMT yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hamas ta fara aiki a Gaza.
Hakan na nufin yaƙin da ak ƙwamawa tsakanin dakarun Isra’ila nda na Hamas zai tsaya sannan kuma za a saki mutanen da Hamas ke garkuwa da su ƴan Isra’ila sannan ita kuma Isra’ila ta saki Falasdinawa da ke gidajen yarinta.
Da farko dai tsagaita wutar ta ɗan samu cikas a safiyar ranar Lahadi bisa abin da Isra’ila ta ce sai Hamas ta fitar da jerin sunayen mutanen da ke hannuta waɗanda za a saki sannan yarjejeniyar ta fara aiki.
Daga bisani ne kuma Hamas a shafinta na X ta saki jerin sunayen wasu mata uku da ta ce na cikin waɗanda za ta saki a zangon farko.
Ita kuma Isra’ila ta fitar da jerin nata na mutum 33 da ta ce su ne take sa ran za su kasance a zangon farko da suka haɗa da wanda ya fi kowanne ƙarancin shekaru.
Ministan tsaron Isra’ilar dai, Itamar Ben-Gvir ya yi murabus daga kujerarsa bisa abin da ya ce miƙa wa Hamas nasara ce. In ji BBC.