A safiyar yau Alhamis an ci gaba da saurarenshari’ar Sheikh Abduljabbar da gwamnatin jihar Kano, a kan shari’ar da a ka fara gabatar wa tun shekarar da ta gabata, bisa zargin kalaman ɓatanci da kuma tunzuri.
Kamar yadda ya gabata, a zaman na yau zai ɗora ne da shedu 4 da masu gabatar da ƙara suka kawo gaban kotu, Farfesa Ahmad Murtala wanda ya zo kotu a matsayin masani kuma kwararre a ilimin hadisi.
A zaman na yau, Lauyoyin masu gabatar da kara karkashin jagorancin, Barista Sa’ida Shu’aibu SAN, sun fara da gabatar da kansu, sannan ya bada damar ci gaba da gabatar da jawabi ga Fafesa Usman Shu’aibu. Sun gabatar wa da kotu shedar kammala digirin farko, na biyu da na uku a kotu, sannan kuma an gabatar da shedar kasancewar shedar Farfesa a jami’ar Bayero dake Kano, da kuma shedar zaman da shugaban sashen Addinin Musulunci na jami’ar Bayero dake Kano.
Shedar ya kuma gabatar da Ijazozin sa ga kotu har guda shida.
”Silsila ce har zuwa manyan littafan hadisai guda 6, da kuma sauran littafan hadisai sanannu, sannan suna bani damar na ruwiaci waɗannan hadisai zuwa Annabi SAW, suna kuma bani damar na karantar dasu na fassara” inji Sheda Farfesa Ahmad Murtala
Bayan gabatar da wadannan takardu na shedar a gaban kotu, kotu ta karɓe su a matsayin sheda abar nuni a cikin Shari’a, inda tayi musu lamba da (Exhibit D, E , F, G, H, I, J1-J6).
Lauyan masu gabatar da kara sun nemi shedar da ya sake fassara hadisan sannan kuma kotu ta shigar da fassarar cikin jawabin da take rubutawa akan shari’ar.
Shedar ya fassara hadisan a kotu, sannan alƙali ya bada hutun minti 30 dan wanda ake ƙara Malam Abdujabbar yayi nazari akai kafin ya yi tambayoyin sa ga shedar. Za a koma shari’ar da misalin karfe 12:00 na rana.