fidelitybank

Yanzu-Yanzu: A na ci gaba da sauraron shaidu a kan shari’ar Abduljabar da gwamnati

Date:

A safiyar yau Alhamis an ci gaba da saurarenshari’ar Sheikh Abduljabbar da gwamnatin jihar Kano, a kan shari’ar da a ka fara gabatar wa tun shekarar da ta gabata, bisa zargin kalaman ɓatanci da kuma tunzuri.

Kamar yadda ya gabata, a zaman na yau zai ɗora ne da shedu 4 da masu gabatar da ƙara suka kawo gaban kotu, Farfesa Ahmad Murtala wanda ya zo kotu a matsayin masani kuma kwararre a ilimin hadisi.

A zaman na yau, Lauyoyin masu gabatar da kara karkashin jagorancin, Barista Sa’ida Shu’aibu SAN, sun fara da gabatar da kansu, sannan ya bada damar ci gaba da gabatar da jawabi ga Fafesa Usman Shu’aibu. Sun gabatar wa da kotu shedar kammala digirin farko, na biyu da na uku a kotu, sannan kuma an gabatar da shedar kasancewar shedar Farfesa a jami’ar Bayero dake Kano, da kuma shedar zaman da shugaban sashen Addinin Musulunci na jami’ar Bayero dake Kano.

Shedar ya kuma gabatar da Ijazozin sa ga kotu har guda shida.

”Silsila ce har zuwa manyan littafan hadisai guda 6, da kuma sauran littafan hadisai sanannu, sannan suna bani damar na ruwiaci waɗannan hadisai zuwa Annabi SAW, suna kuma bani damar na karantar dasu na fassara” inji Sheda Farfesa Ahmad Murtala

Bayan gabatar da wadannan takardu na shedar a gaban kotu, kotu ta karɓe su a matsayin sheda abar nuni a cikin Shari’a, inda tayi musu lamba da (Exhibit D, E , F, G, H, I, J1-J6).

Lauyan masu gabatar da kara sun nemi shedar da ya sake fassara hadisan sannan kuma kotu ta shigar da fassarar cikin jawabin da take rubutawa akan shari’ar.

Shedar ya fassara hadisan a kotu, sannan alƙali ya bada hutun minti 30 dan wanda ake ƙara Malam Abdujabbar yayi nazari akai kafin ya yi tambayoyin sa ga shedar. Za a koma shari’ar da misalin karfe 12:00 na rana.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp