fidelitybank

Yanzu-Yanzu: A na ci gaba da sauraron shaidu a kan shari’ar Abduljabar da gwamnati

Date:

A safiyar yau Alhamis an ci gaba da saurarenshari’ar Sheikh Abduljabbar da gwamnatin jihar Kano, a kan shari’ar da a ka fara gabatar wa tun shekarar da ta gabata, bisa zargin kalaman ɓatanci da kuma tunzuri.

Kamar yadda ya gabata, a zaman na yau zai ɗora ne da shedu 4 da masu gabatar da ƙara suka kawo gaban kotu, Farfesa Ahmad Murtala wanda ya zo kotu a matsayin masani kuma kwararre a ilimin hadisi.

A zaman na yau, Lauyoyin masu gabatar da kara karkashin jagorancin, Barista Sa’ida Shu’aibu SAN, sun fara da gabatar da kansu, sannan ya bada damar ci gaba da gabatar da jawabi ga Fafesa Usman Shu’aibu. Sun gabatar wa da kotu shedar kammala digirin farko, na biyu da na uku a kotu, sannan kuma an gabatar da shedar kasancewar shedar Farfesa a jami’ar Bayero dake Kano, da kuma shedar zaman da shugaban sashen Addinin Musulunci na jami’ar Bayero dake Kano.

Shedar ya kuma gabatar da Ijazozin sa ga kotu har guda shida.

”Silsila ce har zuwa manyan littafan hadisai guda 6, da kuma sauran littafan hadisai sanannu, sannan suna bani damar na ruwiaci waɗannan hadisai zuwa Annabi SAW, suna kuma bani damar na karantar dasu na fassara” inji Sheda Farfesa Ahmad Murtala

Bayan gabatar da wadannan takardu na shedar a gaban kotu, kotu ta karɓe su a matsayin sheda abar nuni a cikin Shari’a, inda tayi musu lamba da (Exhibit D, E , F, G, H, I, J1-J6).

Lauyan masu gabatar da kara sun nemi shedar da ya sake fassara hadisan sannan kuma kotu ta shigar da fassarar cikin jawabin da take rubutawa akan shari’ar.

Shedar ya fassara hadisan a kotu, sannan alƙali ya bada hutun minti 30 dan wanda ake ƙara Malam Abdujabbar yayi nazari akai kafin ya yi tambayoyin sa ga shedar. Za a koma shari’ar da misalin karfe 12:00 na rana.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp