fidelitybank

‘Yan zanga-zanga sun lalata kadarori na Biliyan 5 – Gwamnatin Jigawa

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa ta bayyana cewa an lalata kadarori na Naira biliyan 5 a zanga-zangar da aka yi a fadin kasar a watan Agustan 2024.

Shugaban kwamitin tantance masu zanga-zangar Bello Fanini ne ya bayyana hakan a lokacin da yake gabatar da rahoton kwamitin ga gwamna Umar Namadi a fadar gwamnati dake Dutse babban birnin jihar.

Fanini, ya bayyana cewa kadarorin da aka lalata sun hada da na gwamnatin tarayya, jiha, da kananan hukumomi, da kuma wasu mutane masu zaman kansu da kuma ‘yan kasuwa.

Da yake warware asarar da aka yi, ya ce, “Gwamnatin Jihar Jigawa ta yi asarar da ta kai Naira biliyan 2.8, yayin da Gwamnatin Tarayya da hukumominta suka yi asarar Naira biliyan 1.07. Masu zaman kansu da kamfanoni sun yi asarar ₦707 miliyan, kananan hukumomi sun yi asarar da suka kai miliyan 364, sannan jam’iyyar All Progressives Congress, APC, ta yi asarar sama da miliyan 49.”

Kwamitin ya kuma bayar da shawarwari da dama da nufin hana afkuwar irin haka nan gaba. Daga cikin muhimman shawarwarin akwai bukatar gwamnatin jihar ta biya kamfanoni da daidaikun mutane da suka yi asarar dukiyoyi yayin zanga-zangar.

Da yake mayar da martani, Gwamna Umar Namadi ya nuna jin dadinsa ga kwamitin bisa sadaukarwar da suka yi tare da ba su tabbacin cewa gwamnati za ta yi nazari sosai kan rahoton tare da aiwatar da shawarwarin da aka gabatar.

Idan dai ba a manta ba Gwamna Namadi ne ya kaddamar da kwamitin binciken da zai binciki musabbabin zanga-zangar da aka yi a jihar Jigawa a ranar 1 ga watan Agustan 2024.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp