Gwamnatin jihar Jigawa ta bayyana cewa an lalata kadarori na Naira biliyan 5 a zanga-zangar da aka yi a fadin kasar a watan Agustan 2024.
Shugaban kwamitin tantance masu zanga-zangar Bello Fanini ne ya bayyana hakan a lokacin da yake gabatar da rahoton kwamitin ga gwamna Umar Namadi a fadar gwamnati dake Dutse babban birnin jihar.
Fanini, ya bayyana cewa kadarorin da aka lalata sun hada da na gwamnatin tarayya, jiha, da kananan hukumomi, da kuma wasu mutane masu zaman kansu da kuma ‘yan kasuwa.
Da yake warware asarar da aka yi, ya ce, “Gwamnatin Jihar Jigawa ta yi asarar da ta kai Naira biliyan 2.8, yayin da Gwamnatin Tarayya da hukumominta suka yi asarar Naira biliyan 1.07. Masu zaman kansu da kamfanoni sun yi asarar ₦707 miliyan, kananan hukumomi sun yi asarar da suka kai miliyan 364, sannan jam’iyyar All Progressives Congress, APC, ta yi asarar sama da miliyan 49.”
Kwamitin ya kuma bayar da shawarwari da dama da nufin hana afkuwar irin haka nan gaba. Daga cikin muhimman shawarwarin akwai bukatar gwamnatin jihar ta biya kamfanoni da daidaikun mutane da suka yi asarar dukiyoyi yayin zanga-zangar.
Da yake mayar da martani, Gwamna Umar Namadi ya nuna jin dadinsa ga kwamitin bisa sadaukarwar da suka yi tare da ba su tabbacin cewa gwamnati za ta yi nazari sosai kan rahoton tare da aiwatar da shawarwarin da aka gabatar.
Idan dai ba a manta ba Gwamna Namadi ne ya kaddamar da kwamitin binciken da zai binciki musabbabin zanga-zangar da aka yi a jihar Jigawa a ranar 1 ga watan Agustan 2024.