Wasu masu garkuwa da mutane sun shiga gida-gida sun kashe wata matar aure tare da sace mutum shida a yankin Kwali da ke Abuja.
Wani mazaunin yankin mai suna Yakubu Saidu, ya ce, ’yan bindigar sun fara ne da shiga wasu gidaje biyu suka sace mutum biyu tare da bude wuta cikin daren ranar Talata.
Daga nan suka shiga gidan wani dillalin motoci, amma ba su same shi ba saboda ya tsere, sun yi awon gaba da kannensa maza biyu.
A cewarsa, a ranar Laraba kuma ’yan bindiga sun sake zuwa yankin da misalin karfe 11:23 na dare suka kashe matar a lokacin da take kokarin tserewa.
Ya kuma ce, bayyana cewar an birne matar kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.
Aminiya ta yi kokarin jin ta bakin kakakin ’yan sandan Abuja, DSP Adeh Josephine, amma hakarmu ba ta cimma ruwa ba.