fidelitybank

‘Yan ta’adda sun kashe matar aure da sace mutane 6 a Abuja

Date:

Wasu masu garkuwa da mutane sun shiga gida-gida sun kashe wata matar aure tare da sace mutum shida a yankin Kwali da ke Abuja.

Wani mazaunin yankin mai suna Yakubu Saidu, ya ce, ’yan bindigar sun fara ne da shiga wasu gidaje biyu suka sace mutum biyu tare da bude wuta cikin daren ranar Talata.

Daga nan suka shiga gidan wani dillalin motoci, amma ba su same shi ba saboda ya tsere, sun yi awon gaba da kannensa maza biyu.

A cewarsa, a ranar Laraba kuma ’yan bindiga sun sake zuwa yankin da misalin karfe 11:23 na dare suka kashe matar a lokacin da take kokarin tserewa.

Ya kuma ce, bayyana cewar an birne matar kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.

Aminiya ta yi kokarin jin ta bakin kakakin ’yan sandan Abuja, DSP Adeh Josephine, amma hakarmu ba ta cimma ruwa ba.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp