A safiyar ranar Litinin ne wasu ‘yan ta’adda su ka kai hari shelkwatar ‘yan sandan jihar Abia da ke Umuahia.
Rahotanni na bayyana cewa a yayin harin, an kashe mutum daya da a ke zargin sufeton ‘yan sanda ne.
Wata majiya da ke zaune kusa da ofishin ta bayyana cewa, “Na ji karar harbe-harbe da misalin karfe 1 na safe. Da farko dai, mun yi zaton ’yan sandan da ke ofishin ne ke harbi, domin wani lokaci su kan yi harbi saboda tsoratar da masu kai hari. Da gari ya waye, mun ji an kai hari ne kuma an kashe dan sanda”. inji majiyar.
Sai dai kawo ya zuwa yanzu ba a tantance sunan dan sandan ba a lokacin da a ke gabatar da wannan rahoto.
Mun kuma yi kokarin jin ta bakin mai magana da yawun rundanar ‘yan sandan jihar Abia, Geoffrey Ogbonna, mun kasa samunsa ta layin wayarsa, saboda bai amsa kiran wayar ba ko kuma amsa sakon da a ka aika masa.