fidelitybank

‘Yan sandan Legas sun kama mutane 60 da zargin kisan kai

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas, ta ce ta kama wasu mutane 60 da ake zargi da kisan kai a sassa daban-daban tun daga watan Janairu zuwa Maris 2022.

Ya ce, wadanda aka kama sun hada da wasu mata biyu, daya daga cikinsu ta daba wa saurayin na ta wuka har lahira akan kudi Naira 3,000.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Legas, Abiodun Alabi, wanda ya gabatar da wadanda ake zargin a ranar Litinin, ya ce, an kama mutane 230 a sassa daban-daban na jihar.

Alabi ya samu wakilcin jami’in hulda da jama’a na rundunar, Adekunle Ajisebutu.

Ya ce, an kama 60 daga cikinsu da laifin kisan kai, yayin da 62 kuma aka kama da laifin fashi.

A cewarsa, daga cikin mutane 62 da ake zargi da aikata fashi da makami, 50 daga cikinsu an gurfanar da su a gaban kotu.

“Rundunar ta kuma kama wasu ’yan kungiyar asiri 104 da laifin aikata munanan laifuka. An gurfanar da 98 daga cikinsu a gaban kotu. An kama 12 da laifin fyade/kazanta sannan kuma an kama direbobi 19 saboda karya dokar hanya ta jihar,” inji shi.

Ya kara da cewa, an kwato motoci 15 da aka sace, an kuma dakile ayyukan fashi da makami guda 16, yayin da aka kama motoci 436. A cewar Daily Trust.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp