Rundunar ‘yan sandan jihar Legas, ta ce ta kama wasu mutane 60 da ake zargi da kisan kai a sassa daban-daban tun daga watan Janairu zuwa Maris 2022.
Ya ce, wadanda aka kama sun hada da wasu mata biyu, daya daga cikinsu ta daba wa saurayin na ta wuka har lahira akan kudi Naira 3,000.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Legas, Abiodun Alabi, wanda ya gabatar da wadanda ake zargin a ranar Litinin, ya ce, an kama mutane 230 a sassa daban-daban na jihar.
Alabi ya samu wakilcin jami’in hulda da jama’a na rundunar, Adekunle Ajisebutu.
Ya ce, an kama 60 daga cikinsu da laifin kisan kai, yayin da 62 kuma aka kama da laifin fashi.
A cewarsa, daga cikin mutane 62 da ake zargi da aikata fashi da makami, 50 daga cikinsu an gurfanar da su a gaban kotu.
“Rundunar ta kuma kama wasu ’yan kungiyar asiri 104 da laifin aikata munanan laifuka. An gurfanar da 98 daga cikinsu a gaban kotu. An kama 12 da laifin fyade/kazanta sannan kuma an kama direbobi 19 saboda karya dokar hanya ta jihar,” inji shi.
Ya kara da cewa, an kwato motoci 15 da aka sace, an kuma dakile ayyukan fashi da makami guda 16, yayin da aka kama motoci 436. A cewar Daily Trust.