Rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto ta kama wani ma’aikacin lafiya, Abubakar Hashimu, wanda ya yi wa fitaccen shugaban ‘yan bindigan da ya addabi yankin, Bello Turji, magani a lokacin da sojoji suka raunata shi a wani hari da suka kai shekaru uku da suka wuce.
Da yake jawabi ga manema labarai a ranar Litinin, Mataimakin Sufeto Janar na ‘yan sanda na ayyuka, Ahmed Zaki, ya ce, an kama Hashim ne tare da wasu 36.
Wasu daga cikin wadanda ake zargin sun hada da Musa Kamarawa, Bammi Kiruwa, Zayyanu Abdullahi, Hardo Yunusa da Samuel Chinedu, da dai sauransu.
A cewar sa, an kama mutanen ne tsakanin 20 ga watan Janairu zuwa 29 ga watan Janairu, bayan da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta Operation Sahara Storm ta gano tare da kai sumame sansanonin ‘yan bindigar da ke kananan hukumomin Illela, Rabah, Isa da Goronyo a jihar Sakkwato.
Rundunar ‘yan sandan ta kuma ce, an kama shi ne a wani dakin otel da ke cikin birnin Sakoto, a lokacin da yake jiran kudinsa bayan ya baiwa ‘yan bindigar magunguna da sauran kayan masarufi.