fidelitybank

‘Yan sanda sun kama likitan Bello Turji shugaban ‘yan ta’adda a Sokoto

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto ta kama wani ma’aikacin lafiya, Abubakar Hashimu, wanda ya yi wa fitaccen shugaban ‘yan bindigan da ya addabi yankin, Bello Turji, magani a lokacin da sojoji suka raunata shi a wani hari da suka kai shekaru uku da suka wuce.

Da yake jawabi ga manema labarai a ranar Litinin, Mataimakin Sufeto Janar na ‘yan sanda na ayyuka, Ahmed Zaki, ya ce, an kama Hashim ne tare da wasu 36.

Wasu daga cikin wadanda ake zargin sun hada da Musa Kamarawa, Bammi Kiruwa, Zayyanu Abdullahi, Hardo Yunusa da Samuel Chinedu, da dai sauransu.

A cewar sa, an kama mutanen ne tsakanin 20 ga watan Janairu zuwa 29 ga watan Janairu, bayan da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta Operation Sahara Storm ta gano tare da kai sumame sansanonin ‘yan bindigar da ke kananan hukumomin Illela, Rabah, Isa da Goronyo a jihar Sakkwato.

Rundunar ‘yan sandan ta kuma ce, an kama shi ne a wani dakin otel da ke cikin birnin Sakoto, a lokacin da yake jiran kudinsa bayan ya baiwa ‘yan bindigar magunguna da sauran kayan masarufi.

latest news in lokoja, kogi state

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp